Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
Published: 14th, October 2025 GMT
Tawagar Super Eagles ta Najeriya sun kara da Cheetahs na Jamhuriyar Benin a wasan neman cancantar shiga gasar cin Kofin Duniya ta 2026.
Wasan da suka fafata a filin wasa na Godswil Akpabio da ke Jihar da Uyo ya kasance tamkar mai zafin gaske kuma an nuna bajinta.
Tun kafin a fara wasan, an samu sauye-sauye hudu daga tawagar da ta doke Lesotho, inda Wilfred Ndidi ya hau matsayin kyaftin, yayin da Moses Simon ke shirin yin buga na 85 a wasannin kasa da kasa.
Wasan ya fara da sauri — ina minti na uku kacal, Osimhen ya zura kwallo ta farko bayan Chukwueze yi mika masa. Cheetahs sun yi kokarin farkeaw a minti na 12, amma Calvin Bassey ya dakile harin.
Na yafe wa Maryam Sanda —Mahaifin Bilyaminu Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya AbdullahiA minti na 22, Osimhen ya kusa kara ci, amma dan wasan baya na Benin ya hana shi. Sai dai a minti na 38, Chukwueze ya sake aika masa da wata kwallo, kuma Osimhen bai yi wata-wata ba — ya zura ta biyu! Najeriya 2, Benin 0.
Bayan hutun rabin lokaci, Benin sun fara da matsa lamba, amma Osimhen ya sake daukar hankalin duniya — inda a minti na 51, ya cika hat-trick dinsa! Kwallo ta uku ke nan a hannunsa.
Super Eagles sun ci gaba da matsa lamba, inda suka nemi ci na hudu a minti na 68, amma Ndidi ya kasa cin kwallon da aka buga masa.
A minti na 90 Onyeka ya zura wa Super Eagles kwallon Najeriya na hudu a ragar Jamhuriyar Benin.
Wannan wasan ya nuna cewa Osimhen ba dan wasa bane kawai — jarumi ne, gwarzo ne, kuma jagora ne a fagen kwallon kafa.
Najeriya na kan gaba a wannan fafatawa, kuma alamu na nuna cewa Super Eagles na kan hanya madaidaiciya zuwa Kofin Duniya ta 2026.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaduwa da rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci kuma jagoran Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
Fitaccen malamin ya rasu a Bauchi ranar Alhamis yana da shekaru 101.
Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban AmurkaA cikin wata sanarwa da Kakakin shugaban, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya bayyana Sheikh Dahiru Bauchi a matsayin jagoran da ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa, wa’azi da jagorantar al’ummar Musulmi.
Tinubu ya ce rasuwar malamin ba wai asara ce ga iyalansa da almajiransa kawai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.
“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba ne kuma murya ce ta daidaito da hikima. A matsayinsa na mai wa’azi kuma babban mai fassarar Alƙur’ani mai tsarki, ya kasance mai kira ga zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.
Ya tuna da albarka da ya samu daga marigayin a lokacin shirye-shiryen zaɓen 2023.
Shugaban Ƙasa ya miƙa ta’aziyya ga almajiran malamin a faɗin Najeriya da wajen ƙasar, yana mai kira da su dawwamar da sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, tsoron Allah da kyautatawa ɗan adam.