Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki
Published: 16th, October 2025 GMT
Baba-Ahmed, ya bayyana cewa, abin da danginsa suka fuskanta a hannun masu garkuwa da mutane a bara ya tabbatar masa da cewa rashin tsaro a yanzu yana da nasaba da siyasa.
Ya kuma danganta kisan jama’ar da aka yi wa mabiya Shi’a a Zariya a shekarar 2015 da wani shiri na gwamnati don murƙushe masu sukarsu a wancan lokaci.
Ya jaddada cewa El-Rufai da jam’iyyar APC ba za su iya tserewa daga alhakin halin da Nijeriya ke ciki na rashin tsaro ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Taya Sanata Ahmed Wadada Aliyu Murnar Ranar Haihuwa
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Sanata Ahmed Wadada Aliyu murnar zagayowar ranar haihuwarsa, inda ya bayyana shi a matsayin ma’aikaci mai tawali’u, mai aminci, kuma mai kishin kasa wanda irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban kasa abin a yaba ne.
Shugaban ya yaba wa Sanata mai wakiltar Nasarawa ta Yamma kuma shugaban kwamitin majalisar dattijai kan asusun gwamnati bisa “kishin sa na gaskiya, rikon amana, tsarin kasafin kudi, da dokoki masu tasiri da ke magana kan makomar kasarmu.”
Da yake karin haske kan tarihin Sanata Wadada a Majalisar Dokoki ta kasa, Shugaba Tinubu ya lura cewa “a cikin shekaru biyu kacal a Majalisar Dattawa, kun bambanta kanku a cikin doka, wakilci, da kuma kulawa a matsayin daya daga cikin masu basirar majalisa, mai taka rawa, kuma abin koyi ga matasa masu tasowa.”
Shugaban ya bi sahun al’ummar Nasarawa ta Yamma, ‘yan uwa, abokan arziki, da abokan zaman Sanatan wajen taya shi murna, tare da yi masa fatan Allah ya kara masa karfin gwiwa, da hikima da kuma koshin lafiya domin ya ci gaba da yi wa kasa hidima.
Bello Wakili