“Kusan kullum muna cikin tashin hankali a Shinkafi,” in ji shi.

Mutumin ya kuma zargi gwamnati daga matakin tarayya har zuwa ƙaramar hukuma da zuba wa matsalar ido.

“Hare-haren suna ci gaba a Birnin Yero, Jangeru, Shanawa, da Shinkafi kanta. Ko jiya da safe sun kawo hari sun kama manoma.”

A cewarsa, manoma da dama sun daina zuwa gonakinsu saboda tsoron za a sace su.

Wasu kuma suna zuwa da dare ne kawai don samun ɗan abin da za su ci.

Sai dai, gwamnatin Jihar Zamfara ta ce tana sane da matsalar da jama’ar yankin ke fuskanta, kuma tana ɗaukar matakai don magance ta.

Mai magana da yawun gwamna, Mustafa Jafaru Kaura, ya ce: “Gwamnati tana yin duk abin da ya dace domin ta sharewa jama’a hawaye. Yanzu ma an ba jami’an tsaro da shugabannin ƙananan hukumomi umarni su ɗauki matakin gaggawa.”

Ya kuma jaddada cewa gwamnati tana samun nasara a yaƙi da ‘yan bindigar, yana mai cewa ban da yankin Shinkafi, lamarin ya ragu sosai a sauran sassan Zamfara.

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankin suna fatan wannan tabbacin ba zai zama irin alƙawuran da aka saba ji a baya ba waɗanda ba su taɓa kawo canji mai ma’ana ga rayuwarsu ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara October 15, 2025 Manyan Labarai Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima October 15, 2025 Manyan Labarai Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta October 14, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Rundunar ta kuma yi alƙawarin ci gaba da aikin ceto har sai duk waɗanda aka sace sun kuɓuta kuma an dawo da zaman lafiya a jihar.

Mohammed Gana Alhaji, wanda ya yi magana a madadin al’ummar Patigi, ya gode wa sojojin bisa ƙoƙarinsu na yaƙi da rashin tsaro da kuma kare al’ummar yankin.

A ranar 23 ga watan Satumba, 2025, ‘yan bindiga sun kai mummunan hari wasu ƙauyuka na Patigi, inda suka kashe wata mata mai juna biyu a ƙauyen Matokun, suka yi wa wasu rauni, sannan suka sace mutum takwas.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima October 15, 2025 Manyan Labarai Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta October 14, 2025 Manyan Labarai Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce HKI Tana Jinkirta Neman Gawakin Yahudawa A Gaza
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan