Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke gudanar da ayyukansu a karamar hukumar Toro ta jihar tare da ceto wasu mutane uku da aka sace ba tare da komi ba.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), CSP Mohammed Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Bauchi.

 

A cewar sanarwar, rundunar ‘yan sandan ta samu kiran gaggawa daga wani dan banga da ke kauyen Euga da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar 29 ga watan Satumba, 2025, inda ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi awon gaba da wasu mutane uku wato Idi Umar, Idi Lawan, da Musa Lawal.

 

Wakil ya ce “A martanin da aka mayar, an kaddamar da wani aiki na hadin gwiwa wanda ya hada da rundunar ‘yan sanda ta Toro, Toro Division, Nabordo Division, da kuma jami’an tsaro na cikin gida.”

 

Ya kara da cewa rundunar hadin guiwa ta bin diddigin wadanda ake zargin har zuwa wajen kauyen, inda suka gudanar da wani samame na dabara wanda ya kai ga ceto wadanda lamarin ya rutsa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi.

 

Wadanda aka kama sun hada da Abubakar Usman, Adamu Alo, Abubakar Aliyu, Umar Habu, Abubakar Mamman Abubakar, da Shehu Sambo.

 

Karshen/Alhassan.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Bauchi wasu mutane

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

SP Shiisu ya ce bincike na ci gaba domin gano musabbabin ɓarkewar rikicin.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su ƙara haɗa kai da jami’an tsaro da kuma gaggawar bayar da rahoto idan suka lura da wani abin da zai iya janyo rikici, domin kauce wa zubar da jini.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi October 14, 2025 Manyan Labarai Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa October 14, 2025 Labarai ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa
  • Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato
  • PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa