Aminiya:
2025-10-16@09:07:30 GMT

Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi

Published: 16th, October 2025 GMT

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke wa wani kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafa hukuncin daurin shekaru takwas ba tare da zaɓin tara ba, kan laifin luwadi da ɗan wasan kulob dinsa mai karancin shekaru.

Kotun dai wacce ke ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Musa Dahuru Muhammad a ranar Laraba ta sami kocin mai suna Hayatu Muhammad da aikata laifin.

Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC Majalisar Dattawa za ta tantance Amupitan a ranar Alhamis

Wanda aka yanke wa hukuncin, mazaunin unguwar Sanka ne a ƙaramar hukumar Dala, kuma kotun ta tabbatar da cewa ya aikata laifin har sau biyu a wurare daban-daban.

Da farko dai ya musanta zargin da ake masa.

Sai dai, bayan tabbatar da laifin ba tare da wata shakka ba, lauya mai gabatar da ƙara daga Gwamnatin Jihar Kano, Ibrahim Arif Garba, ya kira shaidu guda biyar da suka ba da shaida a kotu.

A bangarensa, wanda ake tuhuma shi kaɗai ne ya ba da shaida don kare kansa.

Bayan nazarin dukkan shaidun da aka gabatar da kuma bayanan shaidu, Mai Shari’a Dahuru ya tabbatar da cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin kamar yadda aka zarge shi.

Alkalin ya yanke masa hukuncin daurin shekara huɗu kan kowacce tuhuma, kuma ya bayar da umarnin cewa hukuncin zai fara ne tun daga ranar da aka yanke hukuncin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Luwadi

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

 

A yayin shari’ar, wanda ake tuhumar ya musanta zargin, sai dai kotun ta ce masu gabatar da kara sun gabatar da shaida wadda ta gamsar da ita ba tare da wata shakka ba. Mai shari’a Dahiru ya ce laifin ya ci karo da sashe na 284 na kundin laifuffuka, wanda ya haramta yin jima’i ba bisa ka’ida ba, don haka ya yanke wa Hayatu Muhammad hukuncin daurin shekaru hudu a kan kowanne daga cikin tuhumomin biyu, wanda zai fara ne tun ranar da aka kama shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar October 15, 2025 Labarai Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya  October 15, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02% October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ka da a ɗora wa Tinubu laifin rikicin da ke faruwa a PDP — Fayose
  • Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3