Aminiya:
2025-12-01@05:08:45 GMT

’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano

Published: 16th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta kama gungun mutane 11 da ake zargi da kasancewa ’yan fashi da makami da ke addabar matafiya a kan hanyar Katsina zuwa Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Aliyu, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba a Katsina cewa waɗanda ake zargin sun kware wajen tare hanyoyin zuwa Sha’iskawa-Charanchi da Katsina-Kankia-Kano, suna kwace dukiyoyin matafiya.

DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi

Ya bayyana sunayen waɗanda aka kama da suka haɗa da Dikko Ma’aru, Dardau Kabir, Muntari Musa, Labaran Amadu, Usman Ma’aru, Lawal Zubairu, Nasiru Sanusi, da Adamu Kabir.

Sauran sun haɗa da Abdullahi Zubairu, Muhammad Usman da Sale Shehu, dukkaninsu ’yan tsakanin shekaru 21 zuwa 35.

Ya ce, “Nasarar ta samu ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na safe lokacin da aka cafke ɗaya daga cikin gungun yayin da yake ƙoƙarin sayar da wasu kayayyakin da suka yi fashin su, bayan samun sahihin bayanan sirri.

“Bayan samun wannan bayani, jami’anmu sun bi sahu suka kama wanda ake zargin, lamarin da ya kai ga kama sauran ’yan gungun,” in ji shi.

Kakakin ’yan sandan ya ce yayin bincike, an samu agogo guda 80, wayoyi 9 da wuka daga hannun waɗanda ake zargin a matsayin shaidu.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Bello Shehu, ya yaba da ƙoƙarin jami’an da suka gudanar da aikin, tare da nuna godiya ga goyon bayan jama’a.

Aliyu ya rawaito Kwamishinan yana ƙara kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da muhimman bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka a jihar.

Ya kuma ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta gayyaci Yusuf Datti Baba-Ahmed, tsohon abokin takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour a zaben 2023 tare da Peter Obi.

DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed ne a daren Juma’a bisa zargin ci gaba da bayyana ra’ayoyi da take ganin na iya tayar da hankali a Najeriya.

Wata majiyar tsaro ta ce DSS ta daɗe tana bibiyar kalaman Baba-Ahmed a kafafen yada labarai, musamman kan iƙirarin da ya yi na cewa akwai “rikicin kundin tsarin mulki” a Najeriya.

A cewar majiyar, “Kwanan nan Datti Baba-Ahmed ya bayyana a talabijin inda ya zargi kotuna da rundunar sojoji da rashin hana rantsar da Shugaba Bola Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima. Har ma ya yi nuni da cewa rantsar da Tinubu ta bai wa sojoji damar cin mutuncin mutane.

Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika

Ta ƙara da cewa irin waɗannan kalamai na iya haifar da tashin hankali a ƙasar, musamman a irin wannan yanayin siyasa da ake ciki.

Ta ce, “Abin damuwa ne ganin yadda irin wannan magana ta janyo rikice-rikice a wasu ƙasashe kamar Guinea-Bissau. Hukumar tsaro tana ɗaukar wannan da muhimmanci, ba don siyasa ba, sai don kare zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.”

A cewar majiyar, DSS ta yi wannan gayyata ne bisa ƙa’ida, saboda kalaman Datti Baba-Ahmed da suka yi kama da raina ƙoƙarin gwamnati wajen inganta tsaro a matsayin “wasa” na iya tayar da hankalin jama’a da kuma rage amincewa da hukumomin ƙasa.

Ta ce, “Wannan gayyatar ba hukunci ba ne, amma matakin kariya ne domin fayyace niyya, da manufar kalamansa a muhallinsu, da kuma hana fitowar labarai da za su iya haifar da rikici ba tare da an yi niyya ba.”

Har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto, DSS ba ta fitar da wata sanarwa ba, haka kuma Datti Baba-Ahmed bai ce komai a hukumance kan gayyatar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban
  • CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun