Aminiya:
2025-10-16@13:27:03 GMT

’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano

Published: 16th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta kama gungun mutane 11 da ake zargi da kasancewa ’yan fashi da makami da ke addabar matafiya a kan hanyar Katsina zuwa Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Aliyu, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba a Katsina cewa waɗanda ake zargin sun kware wajen tare hanyoyin zuwa Sha’iskawa-Charanchi da Katsina-Kankia-Kano, suna kwace dukiyoyin matafiya.

DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi

Ya bayyana sunayen waɗanda aka kama da suka haɗa da Dikko Ma’aru, Dardau Kabir, Muntari Musa, Labaran Amadu, Usman Ma’aru, Lawal Zubairu, Nasiru Sanusi, da Adamu Kabir.

Sauran sun haɗa da Abdullahi Zubairu, Muhammad Usman da Sale Shehu, dukkaninsu ’yan tsakanin shekaru 21 zuwa 35.

Ya ce, “Nasarar ta samu ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na safe lokacin da aka cafke ɗaya daga cikin gungun yayin da yake ƙoƙarin sayar da wasu kayayyakin da suka yi fashin su, bayan samun sahihin bayanan sirri.

“Bayan samun wannan bayani, jami’anmu sun bi sahu suka kama wanda ake zargin, lamarin da ya kai ga kama sauran ’yan gungun,” in ji shi.

Kakakin ’yan sandan ya ce yayin bincike, an samu agogo guda 80, wayoyi 9 da wuka daga hannun waɗanda ake zargin a matsayin shaidu.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Bello Shehu, ya yaba da ƙoƙarin jami’an da suka gudanar da aikin, tare da nuna godiya ga goyon bayan jama’a.

Aliyu ya rawaito Kwamishinan yana ƙara kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da muhimman bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka a jihar.

Ya kuma ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

 

Dangane da gamsuwa kan nasarorin da Sin ta samu a bangaren raya harkokin mata, kaso 72.8 na masu bayar da amsa a nazarin daga kasashe maso tasowa, sun yaba da kokarin Sin na horar da mata sana’o’i da tallafawa raya harkokin da suka shafe su. Game da nasarorin da aka samu a kasar Sin wajen shigar mata cikin harkokin raya tattalin arziki da zaman takewa da al’adu, da ma gudunmuwar kasar ga raya harkokin mata a duniya, wadanda suka bayar da amsa daga nahiyoyin Afrika da Asia da kudancin Amurka, sun bayyana gamsuwa matuka.

 

Kafar yada labarai ta CGTN da jami’ar Renmin ta Sin ne suka gudanar da nazarin wanda ya shafi muhimman kasashe masu ci gaba da ma kasashe masu tasowa. Sun gudanar da nazarin ne ta hannun cibiyar bincike kan harkokin kasa da kasa a sabon zamani. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta October 13, 2025 Daga Birnin Sin Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin October 13, 2025 Daga Birnin Sin Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba
  • Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
  • Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano