Ma’aikatar raya matasa ta jihar Kwara tare da hadin gwiwar Masu Ruwa da Tsaki don horar da matasa kan amfani da fasahar AI don ganin sun kasance masu amfani da dogaro da kai, da kuma samun fasaha.

 

Da yake jawabi a lokacin da tawagar ta ziyarci ma’aikatar a Ilorin, kwamishinan ci gaban matasa na jihar, Ndanusa Shehu, ya bayyana matakin a matsayin wanda ya dace kuma ya kawo sauyi.

 

A cewarsa Artificial Intelligence wata hanya ce ta tsara makomar aiki a duniya tare da jaddada mahimmancin ganin matasa sun iya amfani da irin wannan kirkirarriyar fasaha.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ci gaba da nuna kyakykyawan manufa na karfafa matasa, tun daga samar da damammaki a fannin tattalin arzikin dijital zuwa saka hannun jari a fannonin fasaha da kasuwanci.

 

A nasa bangaren masu, Daraktan Sadarwa, Sanni Alausa-Issa ya ce shirin ya himmatu wajen inganta shugabanci na gari, hada kan jama’a, da ci gaban matasa ta hanyar ilimi na zamani.

 

ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa

Wasu kudurori guda 3 da ke dauke da bukatun kafa wasu hukumomi 3 sun samu karatu na biyu a zauren majalaisar dokokin jihar Jigawa.

Kudurorin guda 3 sun hada da na kafa Hukumar Samar da Hanyoyin Mota a yankunan karkara, da na kafa Hukumar Samar da Kudade Domin Ayyukan Hanyoyin Mota a yankunan karkara da Kuma na Hukumar Bunkasa Kwazon Malamai ta jihar Jigawa.

A lokacin ya ke gabatar da kudurorin domin neman goyon baya kan bukatar kafa hukumar bunkasa kwazon malamai, mataimakin shugaban masu rinjaye na majlaisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce gwamnatin jihar na da nufin inganta aikin koyarwa ta hanyar kafa hukumar da za ta rinka horas da malamai akai akai.

Da su ke tattaunawa kan wannan batu, wakilan mazabar Kanya Babba da na Fagam da na Sule Tankarar da na Guri, sun lura cewa kafa wannan hukumar zai maye gurbin ayyukan kwalejin horas da malamai da aka rushe a can baya, abin da zai kawo ingancin harkonin koyo da koyarwa a halin yanzu.

Kazalika da ya ke gabatar da kudurin neman goyon baya kan batun kafa hukuma da kuma asusun samar da hanyoyin mota a yankunan karkara, mataimakin shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce daukar wannan mataki zai karfafa yunkurin gwamnatin jihar na inganta harkokin sufuri ga jama’ar karkara.

Da su ke bada gudummawa kan wannan batu, wakilin mazabar Gwaram da na Kiri Kasamma da na Guri da kuma wakilin mazabar Fagam sun bayyana kudurorin biyu a matsayin wata alama da ke nuni da kyakkyawan kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen samar da hanyoyin mota ga yankunan karkara, inda fiye da kaso 60 na jama’ar jihar ke zaune.

Bayan samun goyon baya da gagarumin rinjaye sai aka yiwa kudurorin 3 karatu na 2, daga nan kuma shugaban majalisar dokokin jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya mika kudurori 2 na hanyoyin mota a yankunan karkara ga kwamatin muhalli, yayin da kudurin kafa hukumar inganta kwazon malamai ya je ga kwamatin ilimi mai zurfi da na ilimi matakin farko, wanda dukkan su aka bai wa makonni 4 domin mika rahotannin su.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Inuwa ya naɗa sabbin shugabanni a ma’aikatar lafiya ta Gombe
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa