Hukumar Tsaro ta Najeriya (NSCDC) ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da kare muhimman kadarorin gwamnati a kokarinta na cimma manufar kafa ta.

Kwamandan hukumar a Jihar Kaduna, Malam Panam Musa, ya bayyana haka yayin da yake gabatar da wasu mutane uku da ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati a gaban manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Kaduna.

Kwamanda Musa ya bayyana cewa jami’an hukumar sun cafke wadanda ake zargin ne yayin wani sintiri a kusa da hanyar NNPC da ke Kakau, Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin an kama su ne suna kokarin lalata igiyoyin wutar lantarki na musamman da ke da alaka da wata cibiyar sadarwa a yankin.

A cewarsa, kama su ya biyo bayan sabon umarni daga Babban Kwamandan NSCDC na kasa, Dakta Ahmed Abubakar Audi, wanda ya umurci dukkanin kwamandojin jihohi da su kara tsaurara tsaro da kuma fatattakar masu lalata kadarorin jama’a.

Kwamandan ya tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike, tare da gargadin masu aikata irin wannan laifi da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.

Haka kuma ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba hukumar hadin kai ta hanyar samar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen dakile ayyukan ta’addanci da barnata kadarorin kasa.

Kwamandan ya kara da cewa hukumar za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron muhimman wuraren gwamnati a fadin Jihar Kaduna da ma kasa baki daya.

 

Daga Usman Sani

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 

Gwamnatin Yobe ta bayyana cewa aƙalla mutane 9,854 ne ke ɗauke da cutar AIDS a jihar, kuma dukkaninsu na karɓar maganin ceton rai.

Hukumar ta tabbatar da cewa waɗannan marasa lafiya suna rayuwa cikin ƙoshin lafiya, tare da rage yiwuwar yaɗa cutar ga wasu.

Babban Daraktan Hukumar Kula da Cutar AIDS ta Jihar Yobe (YOSACA), Dakta Jibril Adamu Damazai, ne ya bayyana cewa Yobe na da mafi ƙarancin adadin masu ɗauke da cutar a ƙasar nan da kashi 0.4%, inda ya danganta hakan da dabarun yaƙi da cutar da ake aiwatarwa a jihar.

“Ba mu tsaya a kan wannan nasara ba, muna ƙara ƙoƙari don rage yawan kamuwa da cutar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta kashe sama da Naira miliyan 120 wajen sayen kayan gwaji, abin da ya bai wa ƙungiyoyi damar gano mutanen da ba a san suna ɗauke da cutar ba a cikin al’umma, domin a ba su magani.

A cewarsa, Yobe na kan gaba wajen daidaita dabarun yaƙi da cutar AIDS, musamman ganin yadda ake samun sauye-sauye a kuɗaɗen da ake kashewa a duniya.

Dakta Damazai ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara shirye-shiryen samar da magungunan ƙwayar cutar HIV a cikin gida.

Ya yaba da jajircewar gwamna Mai Mala Buni, wanda ya ƙara kuɗaɗen da ake bai wa hukumar kula da cutar AIDS da kashi 400%, tare da samar da katafaren ofis na dindindin ga hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki