NSCDC Ta Kama Wadanda Ake Zargi Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Kaduna
Published: 17th, October 2025 GMT
Hukumar Tsaro ta Najeriya (NSCDC) ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da kare muhimman kadarorin gwamnati a kokarinta na cimma manufar kafa ta.
Kwamandan hukumar a Jihar Kaduna, Malam Panam Musa, ya bayyana haka yayin da yake gabatar da wasu mutane uku da ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati a gaban manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Kaduna.
Kwamanda Musa ya bayyana cewa jami’an hukumar sun cafke wadanda ake zargin ne yayin wani sintiri a kusa da hanyar NNPC da ke Kakau, Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin an kama su ne suna kokarin lalata igiyoyin wutar lantarki na musamman da ke da alaka da wata cibiyar sadarwa a yankin.
A cewarsa, kama su ya biyo bayan sabon umarni daga Babban Kwamandan NSCDC na kasa, Dakta Ahmed Abubakar Audi, wanda ya umurci dukkanin kwamandojin jihohi da su kara tsaurara tsaro da kuma fatattakar masu lalata kadarorin jama’a.
Kwamandan ya tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike, tare da gargadin masu aikata irin wannan laifi da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.
Haka kuma ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba hukumar hadin kai ta hanyar samar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen dakile ayyukan ta’addanci da barnata kadarorin kasa.
Kwamandan ya kara da cewa hukumar za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron muhimman wuraren gwamnati a fadin Jihar Kaduna da ma kasa baki daya.
Daga Usman Sani
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
Wasu kudurori guda 3 da ke dauke da bukatun kafa wasu hukumomi 3 sun samu karatu na biyu a zauren majalaisar dokokin jihar Jigawa.
Kudurorin guda 3 sun hada da na kafa Hukumar Samar da Hanyoyin Mota a yankunan karkara, da na kafa Hukumar Samar da Kudade Domin Ayyukan Hanyoyin Mota a yankunan karkara da Kuma na Hukumar Bunkasa Kwazon Malamai ta jihar Jigawa.
A lokacin ya ke gabatar da kudurorin domin neman goyon baya kan bukatar kafa hukumar bunkasa kwazon malamai, mataimakin shugaban masu rinjaye na majlaisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce gwamnatin jihar na da nufin inganta aikin koyarwa ta hanyar kafa hukumar da za ta rinka horas da malamai akai akai.
Da su ke tattaunawa kan wannan batu, wakilan mazabar Kanya Babba da na Fagam da na Sule Tankarar da na Guri, sun lura cewa kafa wannan hukumar zai maye gurbin ayyukan kwalejin horas da malamai da aka rushe a can baya, abin da zai kawo ingancin harkonin koyo da koyarwa a halin yanzu.
Kazalika da ya ke gabatar da kudurin neman goyon baya kan batun kafa hukuma da kuma asusun samar da hanyoyin mota a yankunan karkara, mataimakin shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce daukar wannan mataki zai karfafa yunkurin gwamnatin jihar na inganta harkokin sufuri ga jama’ar karkara.
Da su ke bada gudummawa kan wannan batu, wakilin mazabar Gwaram da na Kiri Kasamma da na Guri da kuma wakilin mazabar Fagam sun bayyana kudurorin biyu a matsayin wata alama da ke nuni da kyakkyawan kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen samar da hanyoyin mota ga yankunan karkara, inda fiye da kaso 60 na jama’ar jihar ke zaune.
Bayan samun goyon baya da gagarumin rinjaye sai aka yiwa kudurorin 3 karatu na 2, daga nan kuma shugaban majalisar dokokin jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya mika kudurori 2 na hanyoyin mota a yankunan karkara ga kwamatin muhalli, yayin da kudurin kafa hukumar inganta kwazon malamai ya je ga kwamatin ilimi mai zurfi da na ilimi matakin farko, wanda dukkan su aka bai wa makonni 4 domin mika rahotannin su.
Usman Mohammed Zaria