Aminiya:
2025-10-15@13:55:53 GMT

Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike

Published: 15th, October 2025 GMT

Kotun Babban Majistare da ke Yaba ta bayar da umarnin a tono gawarwakin mutane 10 da gobara ta kashe a ginin Afriland Towers da ke Legas a ranar 16 ga Satumba, 2025, domin a gudanar da bincike a kansu.

Alkalin kotun, Mai shari’a Atinuke Adetunji ce ta bayar da umarnin a ranar Talata bayan ta samu labarin cewa an riga da binne wasu daga cikin waɗanda gobarar ta ritsa da su.

“Mai ƙorafi ya rubuta wa Gwamnatin Jihar Legas don neman izinin tono gawarwakin waɗanda suka mutu, sannan a gudanar da bincike a kansu,” in ji Mai Shari’a Adetunji.

Wannan umarni ya biyo bayan wata wasiƙa daga ofishin babban lauya Femi Falana da aka aike wa Babban Mai Kula da Gawarwaki na Jihar Legas, Mai Shari’a Mojisola Dada, a ranar 29 ga watan Satumba, 2025.

Femi Falana (SAN), ta hannun ofishinsa, ya shigar da ƙorafi ga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Legas, yana neman a gudanar da binciken gawarwaki don gano musabbabin mutuwar da kuma tabbatar da adalci.

A zaman farko na shari’ar, Mai Shari’a Adetunji ta umurci dukkan ɓangarorin da suka halarta da su gabatar da takardun da suka dace kafin zaman kotun na gaba.

Kotun ta kuma gayyaci hukumomi da kamfanoni da suka haɗa da bankin UBA da Hukumar Tara Haraji ta Tarayya (FIRS), Ma’aikatar Kashe Gobara, Afriland Towers, United Capital, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA), Hukumar Tsaro ta Jihar Legas, da sauran masu ruwa da tsaki.

Adetunji ta ƙara da umartar mai ƙorafi da ya tuntubi iyalan waɗanda suka mutu don gano waɗanda ke da niyyar a tono gawar ’yan uwansu domin a gudanar da binciken gawarwaki.

Ta kuma nemi shaidun gani da ido da su bayyana don bayar da bayani kan abin da ya faru.

Lauya Yahaya Atata daga ofishin Falana ya shaida wa kotu cewa zaman na ranar an shirya shi ne don haɗa dukkan masu ruwa da tsaki da kuma fayyace yadda za a gudanar da binciken gawarwaki.

Sai dai alkalin ta lura cewa lauyoyin ba su shirya sosai ba, kuma ta jaddada cewa binciken ba zai ci gaba ba sai an gabatar da dukkan takardun da ake bukata.

Wani lauya mai wakiltar ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu, A. O. Mema, ya shaida wa kotu cewa abokinsa, Peter Ifaranmaye, wanda shi ne manaja a Hukumar Tara Haraji ta Tarayya, an riga da binne shi.

Bayan wannan bayani, alkali Adetunji ta jaddada cewa yin binciken gawarwaki yana da matuƙar muhimmanci.

“Binciken gawarwaki muhimmin abu ne. Ba za mu iya gudanar da bincike ba sai an yi bincike don a gano hakikanin abin da ya faru,” in ji ta.

Kotun ta dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Nuwamba, 2025.

Gobarar ta tashi ne a ginin Afriland Towers, wani katafaren ginin kasuwanci da ke titin Broad a unguwar Legas Island, a ranar 16 ga watan Satumba, inda ta kashe akalla mutane 10 tare da jikkata wasu da dama.

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da sassafe, kuma ta bazu cikin ginin da sauri kafin hukumomin kasha gobara su samu damar shawo kanta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tono gawarwaki a gudanar da bincike binciken gawarwaki Mai Shari a Jihar Legas

এছাড়াও পড়ুন:

Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila

Rahotanni sun bayyana cewa wani ƙazamin faɗa ya barke tsakanin wata ƙabilar Palasɗinawa masu ɗauke da makamai da ƙungiyar Hamas a yankin zirin Gaza bayan an kulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra’ila.

A ranar Litinin da aka fara musayar fursunoni tsakanin Hamas da Isra’ila ne rahotanni suka ɓulla game da faɗan da ya ɓarke tsakanin mayaƙan Hamas da ƙabilar Doghmush a ranar Lahadi.

Wani jami’in Hamas ya bayyana cewa an samu asarar rayuka daga kowane ɓangare a yayin musayar wutan daga misalin ƙarfe 9.30 na dare ranar Lahadi.

Wani mazaunin yankin Sebra da ke Birnin Gaza, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa “Mayaƙan Hamas kimanin 200 ne suka zo aka fafata da su, har sai da suka murƙushe ’yan ƙabilar Doghmush.

Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?

“Wasu ’yan ƙabilar da mayaƙan Hamas sun rasu a yayin artabun,” in ji shi yana mai neman a dakata sunansa saboda dalilan tsaro.

Wata majiya daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta Hamas ta zargi ’yan ƙabilar da yi wa sojojin Isra’ila aiki kuma sun kashe mutane da dama, ta ƙara da cewa an tsare mutum shiga daga danginsu.

Iyalan sun musanta zargin da ake musu na yi wa Isra’ila aiki, amma sun amsa cewa sun kai wasu farmaki ba tare da yin ƙarin haske ba.

Sun kuma zargi Hamas da kai musu hari barkatai, kamar yadda AFP ya ruwaito.

Shugaban kabilar, Abu al-Hassan Doghmush, ya wallafa a Facebook cewa abin “ya kai matakin da in dai kai dan ƙabilarmu ce to a iya harbin ka a ƙafa koma kone maka gida.”

Tun da Hamas ta kwace iko a yankin Gaza a 2007 ta sha fama da kabilu da ƙungiyoyi masu ɗaukar makamai.

A ranar Lahadi ne kungiyar ta sanar da afuwa ga duk kungiyoyin masu laifi, waɗanda ba su aikata kisa a lokacin yaƙin ƙasar da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Ni na nema wa Maryam Sanda yafiya —Mahaifin mijinta
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku