Ni na nema wa Maryam Sanda yafiya —Mahaifin mijinta
Published: 14th, October 2025 GMT
Mahaifin margayi Bilyaminu wanda matarsa Maryam Sanda ta kashe, ya ce shi ne ya roki Shugaba Tinubu ya yafe mata duk da hukuncin kisa da kotu ta yanke mata kan laifin.
Malam Ahmed Bello Isa ya bayyana haka ne yayin ganawa da ’yan jarida, tare da mahaifin Maryam, Alhaji Garba Sanda.
Sun gudanar da taron ’yan jaridar ne bayan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan yafiyar da Shugaban Kasa ya yi mata tare da wasu mutane 174 da ke tsare a gidajen yari bayan an yanke musu hukunci kan manyan laifuka daban-daban.
Aminiya ta ruwaito dangin Bilyaminu ta hannun Dakta Halliru Bello Muhammad, wanda kawu marigayin ne kuma a hannunsa ya taso yana bayyana yafiyar da aka yi wa Maryam Sanda a matsayin kololuwar rashin adalaci da za a yi wa iyalan.
Amma a taron manema labaran, mahaifin na Bilyaminu ya ce dalilin da ya sanya shi roka wa Maryam Afuwa, shi ne don ta rungumi ’ya’yansu biyu da margayin ya bari.
Ya ce a ganinsa, hukuncin kisan da aka yanke mata ba zai dawo masa da dansa ba.
Ya kuma gabatar wa kwafin wata takarda da ke nuna cewa an rubuta ta tun lokacin da ake binciken shari’ar a 2019, yana sanar da Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya cewa a janye batun, saboda ya yafe a matsayinsa na mahaifin mamacin.
Sai dai kuma laifin kisa abu ne da ya shafi hakkin hukuma, don haka hukuma ke da hakkin gurfanarwa.
A shekarar 2023 Kotun Koli ta Tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda kamar yadda Kotun Daukaka Kara ta Abuja da Babbar Kotun Daukaka Kara suka yanke mata da farko.
Tun lokacin aka tura ta zuwa Gidan Yarin da ke Suleja tana zaman jiran a yanke mata hukunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bilyaminu Maryam Sanda Yafiya Maryam Sanda a yanke mata
এছাড়াও পড়ুন:
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
A nata bangare, Sima Bahous ta yabawa ci gaban da Sin ta samu wajen cike gibin fasahohi tsakanin jinsi, da ingiza ci gaban harkokin mata ta kowanne bangare da kare hakkoki da muradun mata.
Ta kuma yi kira ga kasa da kasa su hada hannu tare wajen karfafa gwiwar mata da ‘yan mata su samu ci gaba a zamanin amfani da fasahohi. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA