Taron wanda ya hada jami’ai daga kungiyar AU da jami’an diplomasiyya daga kasashen Afrika da Sin da masana da sauran jami’ai a nahiyar, ya bayyana muhimmancin hada hadin gwiwar Sin da Afrika da shirin nahiyar na TVET. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa October 16, 2025 Daga Birnin Sin Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar? October 16, 2025 Daga Birnin Sin Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin October 16, 2025.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano

Dakarun Sojin Najeriya, sun ceto wasu mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace a Ƙaramar Hukumar Tsanyawa da ke Jihar Kano.

Wannan zuwa ne bayan mazauna Yankamaye Cikin Gari suka sanar da jami’an tsaro cewa ’yan bindiga sun shiga ƙauyensu a daren ranar Juma’a.

’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika

Wannan na cikin wata sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaftin Babatunde Zubairu, ya fitar ranar Lahadi.

Ya ce sojin ƙasa tare da haɗin guiwar sojin sama da ’yan sanda sun garzaya wajen, inda suka yi artabu da ’yan bindigar, sannan suka ceto mutanen da abin ya shafa.

Sai dai Zubairu, ya ce ’yan bindigar sun riga sun kashe wata mata mai shekaru 60 kafin sojoji su isa yankin.

Ya ƙara da cewa bayan harin farko da suka kai, sojojin sun bi sahun ’yan bindigar zuwa yankin Rimaye, inda suka yi musu luguden wuta, wanda hakan ya tilasta musu barin mutanen da suka sace.

Sai dai har yanzu ba a gano inda mutane huɗu da suka sace suke ba.

Bayanai sun nuna cewar bayan ’yan bindigar sun tsere, sun nufi Ƙaramar Hukumar Kankia da ke Jihar Katsina, kuma jami’an tsaro na ci gaba da bibiyarsu.

Kwamandan rundunar, ya yaba da jarumtar  sojojin, ya roƙi jama’a da su riƙa bai wa hukumomin tsaro sahihin bayanai a kan lokaci domin kawar da ’yan bindiga a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji
  • Babban banki Najeriya Ya Tura Dala Miliyan 50 Don Ƙarfafa Kasuwar Musayar Kudade