Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Published: 17th, October 2025 GMT
Taron wanda ya hada jami’ai daga kungiyar AU da jami’an diplomasiyya daga kasashen Afrika da Sin da masana da sauran jami’ai a nahiyar, ya bayyana muhimmancin hada hadin gwiwar Sin da Afrika da shirin nahiyar na TVET. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?
Kafin cimma nasarar hakan, an kwashe sama da shekaru biyu ana gwabza fada da mamaya a Gaza, lamarin da ya haddasa asarar rayuka sama da 67,000, da barnata dukiyoyin da aka kiyasta darajarsu kan kusan dalar Amurka biliyan 70, kana an lalata kusan kaso 90 bisa dari na daukacin gine-ginen dake Gaza, baya ga al’ummun zirin sama da miliyan guda da suka rasa matsugunansu.
Ko shakka babu wannan yanayi ya haifar da wani rauni da zai jima ba a manta da radadinsa a tarihin bil’adama ba. Falasdinawa da bangaren al’ummun Israila sun tafka asarar rayuka, da dukiyoyi, da kudaden kashewa a ayyukan soji, da tabarbarewar alakar sassan kasa da kasa, da ganin baiken yaki daga sassa daban daban.
Sai dai duk da haka, sassan biyu ba su da wata mafita da ta wuce neman wanzar da zaman lafiya. Don haka sassan masu ruwa da tsaki dake da hangen nesa, ke ta maimaita batun kafa kasashe biyu masu cin gashin kai, a matsayin hanya mafi dacewa ta samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin Falasdinu da Isra’ila.
Yanzu dai abun zuba ido a gani shi ne ko yarjejeniyar da aka cimma za ta haifar da cikakkiyar nasarar da ake fata ko a’a. Musamman batun kafuwar kasashe biyu, da baiwa Falasdinawa cikakkiyar damar jagorancin yankinsu, da sake gina Gaza, da bude kafar biyan bukatun jin kai na al’ummar zirin da suka haura miliyan 2.1.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA