Maggi Ya Kaddamar Da Wasanni Na Musamman Domin Watan Ramadan
Published: 17th, March 2025 GMT
Wasan na tare da jarumai da suka hada da Rekiate Ibrahim-AttahRekiya Attah, Ramadan Booth, Rabiu Rikadawa, da sauran jarumai. ‘MAGGI Tales of Ramadan’ yana kunshe da darussa masu kayatarwa da aka tsara na mako 6 wanda zai fara daga farkon watan Ramadan. A yayin kallon wasan za a fuskanci muhimman abin da zai karfafa soyayya a tsakanin al’umma.
A kowanne shafi na labarin zai fito da cikakken abubuwan da suke tattare da darussan watan Ramadan a tsakanin al’umma gaba daya musamman ganin yadda aka kama baki da rana har aka zo yin buda baki da kuma lokacin da yin sahur.
A jawabinta, shugabar vangaren kula da sarrafa MaGGI na kamfanin Nestlé Nigeria, Mrs Rahamatou Palm-Zakari ta bayyana cewa, “Ramadan lokaci ne na rarraba abin da aka mallaka cikin jin dadi da annashuwa a tsakanain al’umma, kuma mun fara wannan taarin ne fiye da shekara goma da suka wuce. Za kuma mu ci gaba da tallafa wa iyalai a cikin al’umma kamar yadda muka saba a baya
Mun kuma yi alkawarin tattaro mutane daga sassan kasa wuri daya, tabbas MAGGI ya yi imanin zaburar da mtane donm su nuna soyayya a tsakanin su musamman wanna lokaci na Ramadan.
MAGGI na daga cikin abubnwan alfarma da kamfanin Nestlé ke sarrafawa. Muna kuma alfahari da cewa al’umma dama har ma da wadanda ba a haifa yanzu za su ci gaba da amfana da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi
Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da aiwatar da ƙarin kashi 70 a albashin ma’aikatan dukkanin makarantun gaba da sakandare na gwamnati da ke jihar.
Sabon tsarin albashin na CONPCASS/CONTEDISS 2024 wanda zai fara aiki daga Oktoban 2025, na daga cikin kokarin gwamnatinsa na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da harkar ilimi a jihar.
Fashewar tankar mai ta yi ajalin mutum 30 a Neja Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsaAmincewar na zuwa ne bayan wani muhimmin zama da aka gudanar tsakanin gwamnan da shugabannin ƙungiyoyin ma’aikatan manyan makarantu (JUTIKS), wanda hakan ya kai ga janye yajin aikin da aka shafe wata guda ana yi.
Taron wanda Ƙungiyar Ƙwadago ta NLC ta shirya kuma aka gudanar a fadar gwamnatin Kaduna, ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyi daga Nuhu Bamalli Polytechnic da ke Zariya, da Kwalejin Ilimi ta Gidan Waya, da kuma Kwalejin Nazarin Jinya da Ungozoma ta Kaduna.
Ana iya tuna cewa, tun a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata ne ma’aikatan manyan makarantun suka tsunduma yajin aikin neman a aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS/CONTEDISS na 2009, da kuma inganta fansho da walwalar ma’aikata gaba ɗaya.
A wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyoyin suka gudanar, sun yaba da jajircewar gwamna Uba Sani wajen kare haƙƙin ma’aikata da bai wa ilimi fifiko.
Haka kuma, sun jinjina wa gwamnatin bisa rage kuɗin makaranta da kashi 50% a dukkanin manyan makarantu, da kuma gyare-gyaren gine-gine da kayan aiki da ake ci gaba da yi.