Leadership News Hausa:
2025-10-17@11:48:52 GMT

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

Published: 17th, October 2025 GMT

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

 

Kafin cimma nasarar hakan, an kwashe sama da shekaru biyu ana gwabza fada da mamaya a Gaza, lamarin da ya haddasa asarar rayuka sama da 67,000, da barnata dukiyoyin da aka kiyasta darajarsu kan kusan dalar Amurka biliyan 70, kana an lalata kusan kaso 90 bisa dari na daukacin gine-ginen dake Gaza, baya ga al’ummun zirin sama da miliyan guda da suka rasa matsugunansu.

 

Ko shakka babu wannan yanayi ya haifar da wani rauni da zai jima ba a manta da radadinsa a tarihin bil’adama ba. Falasdinawa da bangaren al’ummun Israila sun tafka asarar rayuka, da dukiyoyi, da kudaden kashewa a ayyukan soji, da tabarbarewar alakar sassan kasa da kasa, da ganin baiken yaki daga sassa daban daban.

 

Sai dai duk da haka, sassan biyu ba su da wata mafita da ta wuce neman wanzar da zaman lafiya. Don haka sassan masu ruwa da tsaki dake da hangen nesa, ke ta maimaita batun kafa kasashe biyu masu cin gashin kai, a matsayin hanya mafi dacewa ta samar da zaman lafiya mai dorewa tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

 

Yanzu dai abun zuba ido a gani shi ne ko yarjejeniyar da aka cimma za ta haifar da cikakkiyar nasarar da ake fata ko a’a. Musamman batun kafuwar kasashe biyu, da baiwa Falasdinawa cikakkiyar damar jagorancin yankinsu, da sake gina Gaza, da bude kafar biyan bukatun jin kai na al’ummar zirin da suka haura miliyan 2.1.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin October 16, 2025 Daga Birnin Sin Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya October 16, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona October 16, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

‘Yansanda sun kuma samu kuɗi Naira 92,460 da wasu abubuwan maye kamar giya da sauransu.

“Wannan samame sakon gargaɗi ne ga duk masu hannu a fataucin miyagun ƙwayoyi,” in ji SP Adam.

“Yaƙinmu da fataucin miyagun ƙwayoyi yana ci gaba, kuma muna kira ga jama’a su riƙa sanar da mu duk wani abin da suka gani na zargi.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara October 15, 2025 Manyan Labarai Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima October 15, 2025 Labarai Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria  October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta zaftare wa Najeriya guraban Aikin Hajji da sama da kujeru 28,000
  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
  • Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, Isra’ila ta kashe Falasdinawa 3 a Gaza
  • Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Shari’ar Neman Hukunta Isra’ila Kan Batun Gaza
  • Ana Aikin Tsaftace Unguwar Kwankwasiyya Mataki Na biyu
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC