Shugaban Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano (HMB), Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya kai ziyarar ba-zata ta duba aiki a Asibitin karbar Haihuwa na Imamu Wali, na Marmara, da kuma Asibitin Sabon Bakin Zuwo.

Ya kai ziyarar ce domin tabbar bin umarnin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na wucin gadi wajen sauya wuraren gudanar da ayyukan karbar haihuwa da na yara zuwa wasu cibiyoyi daban.

A karkashin wannan umarni, an mayar da sashen haihuwa na Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase zuwa Asibitin Haihuwa na Imamu Wali, yayin da aka mayar da ayyukan yara kyauta da ake yi a Asibitin Yara na Hasiya Bayero zuwa Asibitin Haihuwa na Marmara.

Wadannan canje-canjen sun biyo bayan ci gaba da gyare-gyare da sabunta wadannan asibitoci, wani muhimmin bangare na hangen nesa na Gwamna Yusuf wajen inganta cibiyoyin lafiya a Kano zuwa matakin kasashen duniya da suka ci gaba.

Domin tabbatar da ci gaba da bayar da ayyuka ba tare da tangarda ba, ma’aikatan sassan da abin ya shafa suma an tura su zuwa sabbin wuraren da aka kebe musu.

Yayin ziyarar, Dakta Nagoda tare da daraktoci da ma’aikatan hukumar, ya jaddada muhimmancin bin umarnin gwamnati yadda ya kamata, tare da yabawa shugabanci da ma’aikatan asibitocin da aka ziyarta saboda hadin kai da jajircewarsu.

Ya kara tabbatar da kudirin hukumar wajen tabbatar da cewa bayar da ayyukan lafiya a Jihar Kano zai ci gaba da kasancewa cikin sauki, da inganci, tare da mayar da hankali kan marasa lafiya, duk da gyare-gyaren da ake yi.

 

Daga Khadijah Aliyu

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cibiyoyin Lafiya Gyara

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Amma ya nuna damuwa cewa jinkiri wajen aiwatar da yarjejeniyar da gwamnati ta yi da ASUU na ƙara haifar da rashin jituwa.

Ya roƙi Shugaba Tinubu, da ya sa baki kai-tsaye don kawo ƙarshen rikicin, yana mai gargaɗin cewa jinkiri wajen ɗaukar mataki na iya gurgunta ci gaban da aka samu a fannin ilimi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025 Labarai Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu October 15, 2025 Manyan Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki