Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%
Published: 15th, October 2025 GMT
A ɓangaren hauhawar farashin abinci a watan Satumba na 2025, ya dawo kashi 20.9 cikin 100 a maimakon kashi 37.77 cikin 100 a cikin watan Satumban 2024
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
A zaman na ranar Talata, lauyan masu shigar da kara, Salisu Muhammad-Tahir, ya shaida wa kotun cewa biyu daga cikin wadanda ake tuhumar, Abubakar da Odlyne, ba a samu gabatar da su a gaban mai sharia ba duk da kokarin tilasta musu halartar zaman.
Muhammad-Tahir ya ce “Mun yi iya bakin kokarinmu don tabbatar da kawo su gaban mai shari’a, amma muna neman afuwar kotu,” in ji Muhammad-Tahir, inda ya bukaci alkalin da ya dage sauraron karar tare da tsare Ogugua a gidan yari har sai an gabatar da wadanda ake nema.
Lauyan wanda ake kara, Gideon Uzo, ya roki kotun da ta bar wanda yake karewa ya ci gaba da zama a hannun hukumar hana fataucin mutane ta kasa (NAPTIP) maimakon a tura shi gidan gyaran hali.
Sai dai alkalin kotun, Mai shari’a Amina Adamu-Aliyu, ta ki amincewa da bukatar, inda ta bayar da umarnin a ajiye wadanda ake zargin a gidan gyaran hali. Ta kuma umurci hukumar ta NAPTIP da ta gabatar da mutanen biyu da ba su halarci zaman kotun ba.
An dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 27 ga watan Oktoba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA