Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Bayelsa, Israel Sunny-Goli, ya shawarci tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da ya guji duk wata matsin lambar da wasu ƴan siyasa ke yi masa na ya tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Sunny-Goli ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin halartar shirin Politics Today na tashar Channels, inda yake mayar da martani kan ficewar gwamnan Bayelsa, Douye Diri, daga jam’iyyar PDP.

Ya ce, “Ina ganin Jonathan zai karɓi wannan lamari da zuciya ɗaya saboda mutum ne mai son cigaban jiharsa. Duk da maganganun da ake yi kan zai tsaya takara, bana ina ganin zai yi kuskuren hakan saboda lokaci ya riga ya wuce.

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole Ko Jonathan Zai Iya Ja Da Tinubu A 2027?

Ya ce, tun bayan barin ofis a 2015, tasirin siyasar Jonathan ya ragu, kuma babu wani alamar da ke nuna yana son komawa cikin harkar siyasa kai tsaye. “Bai nuna wata alama ta shiga siyasa ba, tun bayan barin mulki,” in ji shi.

Sunny-Goli ya ƙara da cewa tsohon shugaban ya fi dacewa ya ci gaba da mayar da hankali kan ayyukan zaman lafiya da hulɗa da ƙasashen duniya maimakon komawa cikin rigimar siyasa a gida, musamman a yayin da ake ganin yanayin siyasa a Bayelsa na ya sauya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Siyasa Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu October 16, 2025 Manyan Labarai Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson October 16, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP October 15, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sabon shugaban INEC ya halarci Majalisar Dattawa don tantancewa

Sabon shugaban Hukumar zaɓen Najeriya mai zaman kanta INEC, Joash Ojo Amupitan ya halarci zauren  Majalisar Dattawan Najeriya domin zaman tantance shi.

Amupitan ya halarci zauren Majalisar tare da rakiyar Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Ododo da wasu jami’an gwamnati.

Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano Kashi 16 na ’yan Najeriya ne kawai ke da wajen wanke hannu — UNICEF

Da misalin ƙarfe 12:50 na rana ne, mai baiwa shugaban Ƙasa shawara kan Harkokin Majalisar Dattawa (Majalisar Dattawa), Sanata Abubakar Lado ne ya shigar da sabon shugaban INEC zuwa zauren majalisar dattijai, kuma tuni ya zauna gabanin fara aikin tantance shi.

An bar Amupitan ya shiga zauren majalisar ne bayan shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele ya bayar da umarnin a samar da doka ta 12 domin ba wa baƙi damar shiga zauren majalisar, kuma shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Abba Moro ya mara masa baya.

Matakin na zuwa ne bayan Shugaba Tinubu ya aike wa majalisar wasiƙar buƙatar tantance shi.

A makon da ya gabata ne dai majalisar magabatan ƙasar ta amince da naɗin Farfesa Amupitan a matsayin wanda zai jagoranci hukumar zaɓen INEC.

Bayan tantancewa da amincewar majalisar dattawan, Shugaba Tinubu zai rantsar da shi a matsayin shugaban hukumar ta INEC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa
  • Sabon shugaban INEC ya halarci Majalisar Dattawa don tantancewa
  • Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
  • Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI
  • Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • Juyin mulki: Shugaba Rajeolina ya tsere daga ya rushe majalisa
  • PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai