Leadership News Hausa:
2025-12-01@20:14:45 GMT

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Published: 17th, October 2025 GMT

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Saboda haka, an samu labari daga bangaren Obi cewa, tsohon dan takarar shugaban kasa ba za yi zaben fid da gwani ba da Atiku.

Sai dai kuma, sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya ki cewa uffan kan jita-jitan da ke cewa jam’iyyar ta yanke shawarar gudanar da zaben fid da gwani, wanda hakan ya saba wa tsammanin wasu mambobin, musamman daga bangaren Obi.

A cewar Bolaji, a halin yanzu ADC ba ta mai da hankali kan wane zai tsaya takara a karkashin tutan jam’iyyar ADC a zaben 2027 ba.

“A halin yanzu dai, babu wanda aka tattaunawa kan cewa shi ne sahihin dan takara ko kuma za su gudanar da zaben fitar da gwani. Idan mun kai ga wannan lokaci, za mu yi bayani.

“Wannan ba shi ne abin da muke fifita a wannan lokaci ba. Har yanzu mu jam’iyya ce sabuwa kuma muna mai da hankali kan yadda za mu bunkasa jam’iyyarmu a yanzu. Wannan ya fi muhimmanci a gare mu fiye da magana kan ‘yan takarar shugaban kasa”, in ji shi.

Game da dalilin da ya sa Obi bai yi rajista a matsayin mamba na jam’iyyar ba, Bolaji ya ce, “Mun ce Obi da El-Rufai ba su da katin mamba na ADC tukuna saboda yana son goyon bayan ‘yan takarar jam’iyyarsa ta siyasa ta asali a zaben da ke tafe.”

“A game da Peter Obi, bayan zaben Jihar Anambra ne zai iya zaman cikakken dan jam’iyyar ADC. Idan kuma akwai wani dalili, to ban sani ba.”

A gefe guda kuma, wasu masana siyasa sun yi ikirarin cewa da yiwuwar Obi ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2027 a karkashin jam’iyyar LP wacce take da saukin rikici a cikinta.

Wani masanin siyasa, Dakta Anabi Samuel, ya shaida cewa burin tsayawa takarar shugaban kasa na Obi ba zai samu nasara a jam’iyyar LP ba, sakamakon rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar.

A cewar Anabi, rarrabuwan kai da aka samu saboda shugaban jam’iyyar LP, Julius Abure da wadanda ke cikin tawagarsa za su kawo cikas ga Obi.

“Peter Obi ya samu makiya da yawan gaske a LP, don haka za iyi wuya ya samu damar tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

“Kamar jagoran reshen jam’iyyar, Julius Abure, zai tabbatar cewa ya kawo masa cikas tun daga zaben fid da gwani kuma zai yi wuya su ba shi tikiti kai tsaye.

“Mu kaddara ma ya sami tikitin LP, sai ya fuskanci makiya daga wajen jam’iyyar wadanda za su tabbatar da cewa bai yi nasara ba.

“Idan Obi ba zai iya samun tikitin ADC ba, ya kamata ya dakatar da burinsa na takara,  sai dai idan PDP ta amince za ta ba shi tikitin tsayawa takarar shugaban kasa.

“Akwai jita-jitan da ke cewa yana shirin shiga sabon jam’iyyar siyasa. Ya kamata Obi ya watsar da wannan tunanin. 2027 ba kamar 2023 ba ce, yana bukatar jam’iyya da aka sani da kyakkyawan tsari don samun nasara a zaben 2027”, in ji Anabi.

Ko da yake wasu masu nazarin harkokin siyasa suna ganin cewa Peter Obi ne ya haskaka jam’iyyar LP, sai dai kuma jam’iyyar ta nace cewa tsohon gwamnan ba zai samu tikitin kai tsaye ba a 2027.

Sakataren yada labaran na wani bangare na LP, Obiora Ifoh ya shaida cewa bai dace ba a ba Obi tikitin kai tsaye.

“Za a gudanar da zaben fitar da gwani na jam’iyyarmu. Za a wallafa mukaman da ake da su kuma duk wanda ke da sha’awa zai nema ya bi tsarin zaben fid da gwani yadda ya kamata.

“Ba tsarin dimokuradiyya ba ce na bai wa wani dan takara tikiti kai tsaye,” in ji Ifoh.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tambarin Dimokuradiyya Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe October 10, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole October 10, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya October 10, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: takarar shugaban kasa zaben fid da gwani jam iyyar LP a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa

A ranar nuna goyon baya ga alummar falasdinu shugaban kasar Pakistan Asif Ali zardari ya jinjinawa Alummar falasdinu game da juriya da tsayin Dakar da suka nuna, yace jarumtar da suka nuna ta bude sabon shafin tarihi, don haka gudanar da bincike kan laifukan yaki da HKI ta tafka yana da muhimmanci sosai.

Kasar Pakistan tana da tarihin nuna goyon bayan alummar falasdinu , inda suka nuna goyon bayan alummar falasdinu na hakkin fayyacewa kansu makoma, a kudurin Lahore na shekara ta 1940,don haka wannan kiran na zardari ya kara jaddada tsohon matsayin Pakistan da ya doru kan nuna goyon baya, kwatar yanci da daidaito da kuma adalci.

Kiran da zardari yayi na gudanar da bincike kan laifukan yakin Israila yana nuna irin yadda kasashen musulmi suka damu da rashin daukar matakin doka kan ayyukan da isra’ila ke yi .

Ana sa ran Pakistan za ta ci gaba da fafutukar ganin an baiwa falasdinawa goyon baya a mataki na kasa da kasa, tana bukatar ganin an dakatar da bude wuta ta dindindin yadda za’a isar da kayan agaji, da kuma amincewa da falasdinu a matsayin kasa, kuma Pakistan za ta ci gaba da karfafa sakonninta na diplomasiya tare da bayyana ayyukan isra’ila a matsayin wadanda suka keta doka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro   November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci  A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin  A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa