Aminiya:
2025-12-01@17:05:03 GMT

An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi

Published: 16th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da su a ƙauyen Euga da ke Ƙaramar hukumar Toro a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmed Wakil ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da majiyar PUNCH Metro ta ruwaito ranar Laraba.

Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano

A cewar sanarwar, aikin ceton waɗanda aka kuɓutar ya biyo bayan kiran gaggawa da wani ɗan unguwar ya yi ga hukumar ne.

Wakil ya ce, “A ranar 29 ga Satumba, 2025 da misalin ƙarfe 12:01 na tsakar dare rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta samu kiran gaggawa daga wani ɗan banga na unguwar, inda ya ba da rahoton harin da wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai ga sace wasu maza uku daga ƙauyen Euga, a Ƙaramar hukumar Toro da suka haɗa da: Idi Umar da Idi Lawan da Musa Lawal.”

Ya ƙara da cewa, rundunar ’yan sandan ta yi gaggawar tattara jami’an rundunar ’yan sandan yankin Toro, na babban ofishin jami’an Toro da na ofishin Nabordo, tare da jami’an tsaro na yankin domin kai ɗauki ga lamarin.

“Rundunar haɗin gwiwa ta yi nasarar bin diddigin waɗanda ake zargin zuwa wajen ƙauyen tare da gudanar da aikin ƙwararru wanda ya kai ga ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Wakil ya ƙara da cewa, an kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a wannan lamarin.”

Waɗanda ake zargin sun haɗa da: Abubakar Usman da Adamu Alo da Abubakar Aliyu da Umar Habu da Abubakar Mamman Abubakar da kuma Shehu Samb.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar

Shugaban Ƙungiyar Iyaye na Jami’ar MAAUN, Alhaji Mustapha Balarabe, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa jami’ar ta yanke wasu kuɗi masu yawa domin yaye ɗalibai.

A wata sanarwa da ya fitar tare da sakataren ƙungiyar, Hajiya Habiba Sarki, ya ce koken da aka kai wa PCACC da kuma rahotannin da aka wallafa ba su da tushe.

Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno

Ya bayyana zargin a matsayin yunƙurin ɓata wa jami’ar suna.

Ya ce MAAUN na daga cikin jami’o’in masu zaman kansu mafi sauƙin farashi a Kano, kuma tana ba da ingantaccen ilimi.

“MAAUN na ɗaya daga cikin jami’o’i masu zaman kansu masu sauƙin farashi a Kano, tana ba da ingantaccen ilimi tare da ƙayatattun gine-gine.

“Wasu jami’o’in a jihar suna cajin kuɗin makaranta ninki uku a kan na MAAUN, amma ba a jin kukan kowa game da su. Me ya sa sai MAAUN?

“Idan ɗalibi ya biya kuɗin makaranta na tsawon shekaru huɗu, me ya sa za a ga laifi idan aka nemi ya biya kuɗin yayewa a jami’a mai zaman kanta?

“Wannan ba wani sabon abu ba ne. Wannan batu gaba ɗaya na nuna wata maƙarƙashiya ce da ke nufin ɓata suna da barazana daga wanda ba a san ko waye ba da yake iƙirarin cewa yana kare muradun ɗalibai da iyaye,” in ji shi.

Ya kuma yi tambaya: “Me ya haɗa MAAUN da hukumar PCACC a kan wannan batu?”

A ƙarshe, ya shawarci wanda ya kafa jami’ar da ya ci gaba da jajircewa wajen samar da ilimi mai inganci.

A gefe guda kuma, ya yaba masa saboda ƙin ƙara kuɗin makaranta duk da halin matsin tattalin arziƙi da ya sa wasu jami’o’i ƙara ƙudinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • Najeriya : An yi jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Palasdinu: Kwamandoji Biyu Na Rundunar “Sarayal-Quds” Sun Yi Shahada A Yammacin Kogin Jordan