Aminiya:
2025-10-17@18:04:17 GMT

’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe

Published: 17th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan sandan Jihar Gombe ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka, inda ta gudanar da samame a wata maɓoya da ake zargi da aikata ayyukan ta’addanci da safarar ƙwayoyi a cikin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ta bayyana cewa jami’an da ke ƙarƙashin Gombe Division ne suka gudanar da samamen da misalin ƙarfe 9:00 na dare a ranar Alhamis 10 ga Oktoba, 2025.

Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ’yan sandan Abuja Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo

A cewar sanarwar, jami’an sun kai samamen wata maɓoya da ke bayan jerin shagunan Ƙaramar hukumar Gombe, (Local Government Shopping Complex), inda ake zargin wasu fusatattun matasa ke gudanar da ayyuka irin na ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

“Da zarar matasan suka hangi isowar jami’anmu, suka tsere suka bar kayan ƙwayoyi da sauran haramtattun abubuwan da aka haramta,” in ji DSP Abdullahi.

Daga cikin abubuwan da aka ƙwato akwai nau’ukan miyagun ƙwayoyi kamar Suck and Die, Tramadol da allurarai na Diazepam.

An tura kayan shaida ɗin zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, CP Bello Yahaya ne ya tabbatar da ƙudirin rundunar na ci gaba da tabbatar da Gombe ta zauna lafiya an kuma tsarkake ta daga miyagun ƙwayoyi.

Ya kuma gargaɗi masu aikata laifuka da su daina irin waɗannan ayyuka ko kuma su fuskanci hukuncin doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Miyagun ƙwayoyi miyagun ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Wani daga cikin waɗanda suka ji rauni, wanda shi ne mai kuɗin, ya gode wa jami’an FRSC bisa gaskiya da amana da suka nuna, yana mai cewa abin koyi ne ga kowa.

FRSC ta gargaɗi direbobi da su riƙa kula da motoccinsu akai-akai tare da bin ƙa’idojin hanya domin guje wa aukuwar haɗura.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato October 16, 2025 Manyan Labarai Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson October 16, 2025 Labarai Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari  October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • Za a biya tsofaffin ma’aikatan ƙananan hukumomi kuɗaɗe a Yobe
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa