’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe
Published: 17th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan sandan Jihar Gombe ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka, inda ta gudanar da samame a wata maɓoya da ake zargi da aikata ayyukan ta’addanci da safarar ƙwayoyi a cikin jihar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ta bayyana cewa jami’an da ke ƙarƙashin Gombe Division ne suka gudanar da samamen da misalin ƙarfe 9:00 na dare a ranar Alhamis 10 ga Oktoba, 2025.
A cewar sanarwar, jami’an sun kai samamen wata maɓoya da ke bayan jerin shagunan Ƙaramar hukumar Gombe, (Local Government Shopping Complex), inda ake zargin wasu fusatattun matasa ke gudanar da ayyuka irin na ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.
“Da zarar matasan suka hangi isowar jami’anmu, suka tsere suka bar kayan ƙwayoyi da sauran haramtattun abubuwan da aka haramta,” in ji DSP Abdullahi.
Daga cikin abubuwan da aka ƙwato akwai nau’ukan miyagun ƙwayoyi kamar Suck and Die, Tramadol da allurarai na Diazepam.
An tura kayan shaida ɗin zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, CP Bello Yahaya ne ya tabbatar da ƙudirin rundunar na ci gaba da tabbatar da Gombe ta zauna lafiya an kuma tsarkake ta daga miyagun ƙwayoyi.
Ya kuma gargaɗi masu aikata laifuka da su daina irin waɗannan ayyuka ko kuma su fuskanci hukuncin doka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Miyagun ƙwayoyi miyagun ƙwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
A ranar nuna goyon baya ga alummar falasdinu shugaban kasar Pakistan Asif Ali zardari ya jinjinawa Alummar falasdinu game da juriya da tsayin Dakar da suka nuna, yace jarumtar da suka nuna ta bude sabon shafin tarihi, don haka gudanar da bincike kan laifukan yaki da HKI ta tafka yana da muhimmanci sosai.
Kasar Pakistan tana da tarihin nuna goyon bayan alummar falasdinu , inda suka nuna goyon bayan alummar falasdinu na hakkin fayyacewa kansu makoma, a kudurin Lahore na shekara ta 1940,don haka wannan kiran na zardari ya kara jaddada tsohon matsayin Pakistan da ya doru kan nuna goyon baya, kwatar yanci da daidaito da kuma adalci.
Kiran da zardari yayi na gudanar da bincike kan laifukan yakin Israila yana nuna irin yadda kasashen musulmi suka damu da rashin daukar matakin doka kan ayyukan da isra’ila ke yi .
Ana sa ran Pakistan za ta ci gaba da fafutukar ganin an baiwa falasdinawa goyon baya a mataki na kasa da kasa, tana bukatar ganin an dakatar da bude wuta ta dindindin yadda za’a isar da kayan agaji, da kuma amincewa da falasdinu a matsayin kasa, kuma Pakistan za ta ci gaba da karfafa sakonninta na diplomasiya tare da bayyana ayyukan isra’ila a matsayin wadanda suka keta doka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci