Aminiya:
2025-11-14@21:16:25 GMT

Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe

Published: 15th, October 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta ƙaddamar da bincike kan ƙaruwar koke-koken ’yan Najeriya kan yawan cire musu kuɗaɗe ba tare da bayani ba daga asusun ajiyarsu da bankunan kasuwanci ke yi.

Wannan mataki ya biyo bayan amincewa da wani ƙuduri da ɗan majalisa Hon. Tolani Shagaya (APC, Kwara) ya gabatar, inda ya nuna damuwa kan abin da ya kira “cire kuɗaɗe ba tare da bayani ba, da kuma yawan kuɗaɗen da ake karɓa ba bisa ka’ida ba,” duk da dokokin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya kafa.

An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna Kofin Duniya: Da sauran rina a kaba duk da Najeriya ta ci Jamhuriyar Benin 4-0

Yayin gabatar da ƙudurin a zaman majalisa ranar Talata, Shagaya ya ce duk da cewa ana sa ran bankuna su bayar da muhimman ayyukan kuɗi cikin farashi mai sauƙi, yawancin ’yan Najeriya na fuskantar cire kuɗaɗe da dama.

Ya ce cire kudade kamar kuɗin saƙon SMS, kuɗin gyaran kati, kuɗin kula da asusu, kuɗin canja wuri tsakanin bankuna, harajin tambari, da wasu cire-cire da ba a bayyana ba, da dama daga cikinsu ma ana maimaita su ko ba a bayyana su yadda ya kamata ba.

Ya nuna damuwa cewa irin waɗannan halaye na ci gaba da faruwa duk da cewa CBN ya fitar da ƙa’idoji masu bayyani kan yadda za a sarrafa kuɗaɗen da bankuna ke karɓa, amma yawancin bankuna na take waɗannan ƙa’idoji ba tare da jin tsoron hukunci ba.

“Irin waɗannan halaye na zalunci ya fi shafar ’yan kasuwa, masu ƙaramin karfi, ɗalibai, da ƙungiyoyin da ke cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.

“Idan ba a gaggauta bincike da ɗaukar mataki ba, za su ci gaba da rage amincewar jama’a ga tsarin banki, su ƙara yawan waɗanda ba su da damar shiga harkokin kuɗi, kuma su lalata manufofin CBN na faɗaɗa damar shiga tsarin kuɗi,” in ji shi.

Bayan amincewa da ƙudurin, Majalisar ta bukaci CBN da ya fitar da jerin kuɗaɗen da aka amince da su cikin sauƙi ta yadda kowa zai fahimta, tare da tabbatar da aiwatar da hukunci ga bankunan da suka karya doka.

’Yan majalisar sun kuma bukaci babban bankin ƙasa da ya kafa wata hanya mai sauƙi da inganci don karɓar koke-koke daga abokan ciniki da suka fuskanci cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba ko fiye da kima.

Bugu da ƙari, Majalisar ta bukaci Hukumar Kare Masu Sayen Kaya (FCCPC) da sauran hukumomin da suka dace da su fara yaɗa shirye-shiryen wayar da kan jama’a a faɗin ƙasa don sanar da su haƙƙinsu dangane da kuɗaɗen da bankuna ke karɓa.

Ƙudurin ya kuma umarci Kwamitin Majalisa kan Dokokin Banki da Harkokin Bankuna da su gayyaci CBN da manyan bankunan kasuwanci don bayyana dalilan da ke sa ake ci gaba da cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba.

An umurci kwamitocin da su dawo da rahoto ga Majalisar cikin makonni huɗu domin ɗaukar matakin da ya dace na gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cire kuɗaɗe kuɗaɗen da kuɗaɗe ba

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Dillalin Makamai A Taraba

A ci gaba da aikace-aikacen yaki da ta’addanci da laifuffuka a fadin Jihar Taraba karkashin Operation Lafiya Nakowa, sojojin Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya / Sashen 3 na Operation Whirl Stroke (OPWS) sun samu nasarar kama wani wanda ake zargin dillalin makamai, tare da kwato makamai da harsasai daga hannunsa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Lieutenant Muhammad, Mai Rikon Mukamin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar 6, ya sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, bisa sahihan bayanan leƙen asiri da aka samu, a ranar 12 ga Nuwamba, 2025, sojojin suka kai samame a kauyen Shagada, karkashin gundumar Namnai a Karamar Hukumar Gassol, Jihar Taraba. Samamen ya haifar da kama wani mutum mai suna Abdulmudallabi Audu, mai shekaru 25, wanda aka same shi da makamai da harsasai.

Kayan da aka gano daga hannun wanda ake zargin sun haɗa da Bindiga samfurin AK-47 guda ɗaya da kurtun harsasai AK-47 guda biyu da kuma Harsasai guda 53 masu tsawo mita kusan 8.

A yanzu haka, wanda ake zargin tare da kayan da aka kwato suna tsare a hedkwatar Runduna ta 6 domin bincike da shirin gurfanarwa a kotu.

Kwamandan Rundunar 6, Brigadier Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin bisa ƙwarewa, jajircewa, da saurin mayar da martani ga bayanan sirri da ake samu.

Janar Uwa ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aikace-aikace masu ƙarfi a duk fadin Taraba domin tabbatar da zaman lafiya, tsaro, da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a Arewa maso Gabas da yankunan makwabta.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da bayanai sahihai akan lokaci ga jami’an tsaro domin taimakawa wajen kassara masu aikata laifuka da farfaɗo da cikakken zaman lafiya a jihar.

Sani Sulaiman/Jalingo

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Dillalin Makamai A Taraba
  • Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn
  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu
  • Yadda muka daƙile yunƙurin tsige Akpabio daga shugabancin Majalisa – Orji Kalu