Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe
Published: 15th, October 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta ƙaddamar da bincike kan ƙaruwar koke-koken ’yan Najeriya kan yawan cire musu kuɗaɗe ba tare da bayani ba daga asusun ajiyarsu da bankunan kasuwanci ke yi.
Wannan mataki ya biyo bayan amincewa da wani ƙuduri da ɗan majalisa Hon. Tolani Shagaya (APC, Kwara) ya gabatar, inda ya nuna damuwa kan abin da ya kira “cire kuɗaɗe ba tare da bayani ba, da kuma yawan kuɗaɗen da ake karɓa ba bisa ka’ida ba,” duk da dokokin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya kafa.
Yayin gabatar da ƙudurin a zaman majalisa ranar Talata, Shagaya ya ce duk da cewa ana sa ran bankuna su bayar da muhimman ayyukan kuɗi cikin farashi mai sauƙi, yawancin ’yan Najeriya na fuskantar cire kuɗaɗe da dama.
Ya ce cire kudade kamar kuɗin saƙon SMS, kuɗin gyaran kati, kuɗin kula da asusu, kuɗin canja wuri tsakanin bankuna, harajin tambari, da wasu cire-cire da ba a bayyana ba, da dama daga cikinsu ma ana maimaita su ko ba a bayyana su yadda ya kamata ba.
Ya nuna damuwa cewa irin waɗannan halaye na ci gaba da faruwa duk da cewa CBN ya fitar da ƙa’idoji masu bayyani kan yadda za a sarrafa kuɗaɗen da bankuna ke karɓa, amma yawancin bankuna na take waɗannan ƙa’idoji ba tare da jin tsoron hukunci ba.
“Irin waɗannan halaye na zalunci ya fi shafar ’yan kasuwa, masu ƙaramin karfi, ɗalibai, da ƙungiyoyin da ke cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.
“Idan ba a gaggauta bincike da ɗaukar mataki ba, za su ci gaba da rage amincewar jama’a ga tsarin banki, su ƙara yawan waɗanda ba su da damar shiga harkokin kuɗi, kuma su lalata manufofin CBN na faɗaɗa damar shiga tsarin kuɗi,” in ji shi.
Bayan amincewa da ƙudurin, Majalisar ta bukaci CBN da ya fitar da jerin kuɗaɗen da aka amince da su cikin sauƙi ta yadda kowa zai fahimta, tare da tabbatar da aiwatar da hukunci ga bankunan da suka karya doka.
’Yan majalisar sun kuma bukaci babban bankin ƙasa da ya kafa wata hanya mai sauƙi da inganci don karɓar koke-koke daga abokan ciniki da suka fuskanci cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba ko fiye da kima.
Bugu da ƙari, Majalisar ta bukaci Hukumar Kare Masu Sayen Kaya (FCCPC) da sauran hukumomin da suka dace da su fara yaɗa shirye-shiryen wayar da kan jama’a a faɗin ƙasa don sanar da su haƙƙinsu dangane da kuɗaɗen da bankuna ke karɓa.
Ƙudurin ya kuma umarci Kwamitin Majalisa kan Dokokin Banki da Harkokin Bankuna da su gayyaci CBN da manyan bankunan kasuwanci don bayyana dalilan da ke sa ake ci gaba da cire kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba.
An umurci kwamitocin da su dawo da rahoto ga Majalisar cikin makonni huɗu domin ɗaukar matakin da ya dace na gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cire kuɗaɗe kuɗaɗen da kuɗaɗe ba
এছাড়াও পড়ুন:
Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.
A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.
Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a KadunaYa ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.
Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.
Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.
Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.
Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.
Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.