2025-10-15@21:37:33 GMT
إجمالي نتائج البحث: 8102

«idan aka kwatanta da watan»:

(اخبار جدید در صفحه یک)
    Dubun dubatar mutane ne suka fito zanga-zanga jiya Asabar a sassan wasu ƙasashen Turai domin nuna goyon baya ga Falasɗinawa, tare da kiran a kawo ƙarshen yaƙin Gaza. Rahotanni sun ce masu zanga-zangar sun kuma buƙaci a saki masu fafutuka da ke cikin ayarin jiragen ruwan nan da ke hanyar kai kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza. Rundunar Sojin Nijeriya ta cafke jami’anta 16 kan saɓa ƙa’idar aiki Fitaccen ɗan jarida a Kano, Aliyu Abubakar Getso ya rasu ’Yan sanda a birnin Rome na Italiya sun ce kimanin mutane dubu 250 ne suka fito zanga-zanga a rana ta huɗu a jere, bayan da Isra’ila ta kama ayarin jiragen ruwa 45 da ke ƙoƙarin isa Gaza domin kai wa al’umma agaji...
    Daga baya jami’an ‘yansanda suka ceto basaraken bayan sun tare hanyar da ‘yan bindigar ke bi wajen tserewa.   Yayin da ake yi masa tambayoyi, Yellow ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, kuma ya amince ya karɓi ₦6,000 a matsayin kason sa na kudaden da aka sace. Ya kuma bayyana sunayen sauran abokan aikinsa, wadanda tuni wasu daga cikinsu suka gamu da ajalinsu a batakashin da suka yi da hukumomin tsaro. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da cafke wasu manyan jami’anta guda 16 kan zarginsu da rashin ɗa’a da kuma saɓa ƙa’idar aiki. Darekan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron soji, Birgediya Janar Tukur Gusau ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa ta musamman da ya fitar a ranar Asabar. Fitaccen ɗan jarida a Kano, Aliyu Abubakar Getso ya rasu Ban taɓa cewa Buhari yana da alaƙa da Boko Haram ba — Jonathan Duk da cewa sanarwar ba ta bayyana sunayen jami’an da aka kama ba, sai dai ta ce binciken da aka gudanar ya danganta laifuffukan su da gaza cin jarabawar samun ƙarin girma da kuma wasu dalilai na daban. Kakakin sojin ya ce ana tsare da waɗannan jami’ai saboda tuhumar...
    Ya kara da cewa, “Ba a bar mu mun yi noma ba, kuma ana kwace mana kayanmu, Haƙurin mutane ya fara kaiwa bango.”   “Mutane suna rayuwa cikin tsoro, waɗannan miyagu suna barazanar hana mu girbin amfanin gonakinmu.   “Akwai wata ƙungiya da ake kira Lakurawa da kowa ke tsoro – karfinsu a yankin yana ƙaruwa.” Haruna ya ƙara da cewa. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Iran ta yi kira ga kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ta dauki matakin haramtawa Isra’ila shiga harkokin wasanni na kasa da kasa. A cikin wata wasika da ya aike zuwa ga ministocin harkokin wasanni na kasashe 57 na kungiyar ta OIC, ministan wasanni da matasa na kasar Iran Ahmad Donyamali ya bukaci takwarorinsa da su hada karfi da karfe wajen ganin an kawar da Isra’ila daga wasannin kasa da kasa. Mista Donyamali ya yi kira da a kafa kungiyar wasanni ta kasashen musulmi domin neman kwamitin Olympics na kasa da kasa (IOC) ya dakatar da gwamnatin Isra’ila a gasar wasannin duniya. A cikin wasikar tasa, ya jaddada cewa gwamnatin Isra’ila ta keta yarjejeniya wassanin Olympics da duk...
    Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qassem ya tabbatar da cewa Palasdinawa ne kawai suke da hakkin shawara kan makomar yankin zirin Gaza, da kuma abin da suke ganin ya dace da hakan, yana mai jaddada cewa mika wuya ba dabi’ar Falastinawa ba ce. Dangane da shirin shugaban Amurka Donald Trump kan zirin Gaza, Sheikh Qassem ya bayyana cewa shrin yana tattare da hadari, inda ya kara da cewa an gabatar da shi ta wani salo na musamman ga wasu kasashen Larabawa. An yi ganawa tsakanin Trump da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, kuma an yi canje-canje a cikin da suka yi daidai da mahangar Isra’ila a cikin bayanin, sabanin abin da aka sanar da kasashen larabawa da na musulmi tun...
    Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya musanta maganganun da ake yaɗawa cewar ya ce tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, yana da alaƙa da Boko Haram. Jonathan, ya yi wannan bayani ne kan cewar an fahimci bayaninsa a baibai, a taron ƙaddamar da littafin tsohon Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Lucky Irabor. ’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da sace hakimi a 2023 a Kano Isra’ila ta kai hare-hare a Gaza duk da kiran Trump na tsagaita wuta A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ikechukwu Eze, ya fitar, Jonathan ya ce ba a fahimci ainihin kalamansa ba. “Ofishin Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya lura da rahotannin karya da ke yawo a wasu kafafen labarai wai Jonathan...
    BICTOR IKPEBA – 1997 Dan wasan Nijeriya Bictor Ikpeba, ne da ake yi wa lakabi da suna “Prince of Monaco,” Ikpeba ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Monaco ta samu nasarar lashe kofin Ligue 1 ta Faransa. Danwasan ya samu kuri’a 2, inda ya kare a mataki na 32 a cikin jerin wadanda suka samu karramawa a shekarar ta 1997. ADEMOLA LOOKMAN – 2024 A kakar bara, wanda ya lashe gwarzon dan kwallon kafa na Afirka, Ademola Lukman, wanda a lokacin yake buga wasa a kungiyar Atalanta ne ya zo na 14 a bikin karramawar. Lookman ya lashe gasar Europa da Atalanta, inda ya zura kwallo uku rigis a raga, sannan ya taka rawar gani sosai a...
    Wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Fu Cong ya wakilci kasashe masu ra’ayoyi kusan iri daya wajen yin jawabi kan takunkumin da aka saka daga bangare daya, a gun kwamiti na uku na babban taron MDD cewa, a yayin da aka cika shekaru 80 da kafuwar MDD, tilas ne kasa da kasa su maida hankali da kara yin hadin gwiwa don kin amincewa da wannan takunkumi da ake kakabawa ba bisa doka ba. Fu Cong ya bayyana cewa, a halin yanzu, ana samun ra’ayin bangare daya da ka’idar mai karfi ya samu fifiko a duniya, sannan ana samun takunkumin da aka saka daga bangare daya. Kasashe masu tasowa da jama’arsu suna fama da takunkumin, wanda ya saba wa daidaiton...
    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama wani mutum da ake zargi da hannu wajen sace Hakimin Garin Garun Babba, Alhaji Abdulmumini Mudi Zakari, a shekarar 2023. Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Asabar. Gwamna Namadi ya raba wa mata 1,400 tallafin kayan ɗinkin hula a Jigawa Dalilin da ya sa na tsere Kamaru bayan Boko Haram ta ƙone fadata a Borno — Basarake Ya ce an kama wanda ake zargin mai suna Usman Lawan Baba, wanda aka fi sani da “Yellow,” mai shekara 27, a ranar 2 ga watan Oktoba, 2025, a garin Dakatsalle da ke Ƙaramar Hukumar Bebeji. Wanda ake zargin tare da wasu sun sace hakimin sannan suka...
    Sojojin HKI sun bada sanarwan cewa zasu fara shirin aiwatar da shirin shugaban Trump na tsagaita buduewa juna wuta a Gaza. Da kuma batun musayar fursinoni gaba daya da kungiyar Hamas. Shafin yanar gizo na labarai Arab News na kasar Saudia ya bayyana cewa a jiya da yamma ne kungiyar Hamas ta bayyana cewa ta amince da tsagaita wuta tsakaninta da HKI wanda shugaban kasar Amurka Donal Trump ya gabatar. Kungiyar ta bayyana cewa ta amince da wasu sassa na yarjeniyar amma sai an tattauna kan wasu. Wata majiyar sojojin yahudawan ta bayyana cewa shuwagabannin kasar sun basu umrnin dakatar da kai hare- hare kan falasdinawa a Gaza. Wannan sanarwan ta zo sa’o’ii kadan bayan da shugaban Amurka ya umurci...
    An kuma ce duk wani bincike da aka yi a sashen karatu da kundin tsofaffin ɗalibai bai nuna sunansa ba. Wannan binciken ya jefa shakku kan sahihancin takardun ilimin ministan, tare da tayar da ƙura kan yadda gwamnati ke tantance waɗanda ake bai wa manyan muƙaman gwamnati. Duk da cece-ku-ce da ake yi, har yanzu Nnaji bai mayar da martani ba, haka kuma fadar Shugaban Ƙasa ta ƙi ta ce komai kan lamarin. Wannan na zuwa ne a lokacin da ake tambaya kan yadda ake ɗaukar nauyin masu riƙe da muƙamai a gwamnatin Tinubu, musamman kan tsarin tantancewa kafin a ba su manyan muƙamai. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai...
    Burgediya JanarEsma’il Qa’ani babban kwamnadan dakarun “Qudus'” IRGC a nan Iran ya bayyana cewa kungiyar Hamas ta boye ranar fara yakin tufanul Aksa har shugaban kungiyar Shahid Isma’il Haniyya da shahida Nasarallah duk basu san da lokaci fara yakin ba, sai suka ji an fara. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Qa’ani yana fadar haka, a jiya jumm’a a hirar da aka yi da shi a tashar talabijin ta cikin gida a nan Iran. Ya kumakara da cewa a lokacinda aka fara yakin shugaban kungiyar ta Hamas yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Iraki, yana dawowa ne ya ji labarin fara shi. Janar Qa’ani ya kara da cewa, amma  duk da haka, shahida Nasarallah ya zauna...
    Hukumar sararin samaniya ta kasar Iran ta bada sanarwan shirin cilla tauraron dan’adam a cibiyar cilla taurarin dan’adam na Chabahar tare da amfani da sandarerren makamashi. Kamfanin ndillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban hukumar Hassan Salarieh yana fadar haka a yau Asabar ya kuma kara da cewa, an kammala bangare na farko na cibiyar cilla taurarin yan’adam na Chabahar kuma hukumar ta fara shirin amfani da sandarerren makamashi don cillan taurarin yan’adam da suke gabanta, wadanda a shirye suke a cillasu. Salarieh y ace a halin yanzu akwai tauraron dan Adam mai suna Pars-2 da ke jiran  cillawa, sannan hukumar zata ci gaba da aiki a bangare na 2 na cibiyar don kammala aikin cibiyar cilla tararin...
    A ranar 3 ga watan ne hukumar ciniki ta duniya (WTO) ta gudanar da taron shekara-shekara na majalisar kula da harkokin cinikayya karo na uku a birnin Geneva na kasar Switzerland. Kasar Sin ta yi amfani da wannan dama domin daidaita wannan batu, inda ta fallasa tare da sukar matakin “harajin ramuwa” na Amurka daga bangare guda da gitta kariyar cinikayya, inda ta yi nuni da cewa, matakan kakaba harajin da Amurka ta dauka sun haifar da illa ga harkokin cinikayyar duniya, kana ta bukaci Amurka ta mutunta ka’idojin WTO, tare da yin aiki da dukkan bangarori don karfafa gudanar da harkokin kasuwancin duniya cikin kwanciyar hankali ba tare da tangarda ba. Membobi irinsu Indiya, Brazil, Masar da Pakistan sun...
    Shugaban cibiyar fasaha da kere-kere ta Pardis a nan Tehran ya bada sanarwan cewa, wakilai daga kasashe 65 ne suka bayyana anniyarsu ta halattan gasar fasahar kere-kere ta shekara ta 2025 a cibiyarsa. Kamfanin dilancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Mehdi Saffaari –Nio yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa gasar ta dai-dai kun mutane, wadanda zasu gwada korewarsu da kuma fasahar da suke da ita a gasar wacce za’a gudanar daga ranar 27-30 ga watan Octoba damukeciki a nan Tehran. A taron yan jaridun da ya kira don bada wannan sanarwan Mehdi Safaari-nio ya ce mafi yawan mahallata gasar matasa ne musamman daliban makarantu wadanda suke son gwada korewarsu da kumailminsu.  Kuma a...
    Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya ƙaddamar da shirin tallafa wa mata 1,400 da kayan sana’ar ɗinkin hula domin bunƙasa harkokin kasuwancinsu. A wajen bikin raba kayan, Gwamna Namadi ya ce ɗinkin hula tsohuwar sana’a ce da mata suka gad tun daga iyaye da kakanni, wadda ke taimaka musu wajen dogaro da kai da kuma kula da iyalansu. ’Yan sanda sun bindige Lakurawa 3 har lahira a Kebbi Dalilin da ya sa na tsere Kamaru bayan Boko Haram ta ƙone fadata a Borno — Basarake Waɗanda suka ci gajiyar wannan shiri na farko, sun fito daga ƙananan hukumomi bakwai na masarautar Dutse, waɗanda suka haɗa da Dutse, Kyawa, Birnin Kudu, Buji, Gwaram, Jahun da Miga. Gwamnan ya ce da...
      Me Hakan Ke Nufi Ga Tawagar Nijeriya? Ga Yadda Tsayuwar Rukunin C Yake A ranar 9 ga watan Satumba ne tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta tashi da kunnen doki a wasan da ta buga da tawagar ta Afirka ta Kudu a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya. Bayan wasan ne kasar Afirka ta Kudu ta kara zama a saman teburi da maki 17 cikin wasa takwas da ta buga a Rukunin C. Tawagar Jamhuriyar Benin ke biye mata da maki 14, sai kuma Nijeriya da ke mataki na 3 da maki 11. Sai dai kuma Nijeriya ta kasance tana da maki daya ne da na Rwanda da ke mataki na 4, sai kuma kasar Lesotho da...
    Ana ta rade-radin an baki sarauta, shin mene ne gaskiyar maganar? Alhamdulillah, maganar an bawa Zahra’u sarauta ba karya ba ne, hakkun haka ne an ba ni sarauta.   Mutane za su so su ji, shin daman Haj. Zahra’u ‘yar Ghana ce, tana da sarauta a Ghana? A’a! Ni ba ‘yar Ghana ba ce, ba abin da na hada da Ghana, sai dai so da yarda, saboda ma’abota kallon finafinan hausa ne. Ni kuma ina cikin wannan masana’anta ta finafinan hausa, musamman Dadin Kowa na Arewa24. Alhamdulillah Arewa24 ta sa sunanmu ya tafi a duniya. Ta yi mana riga ta yi mana wando babu abin da ba ta yi mana ba, domin dalilin fuskanmu da ta tafi ake kaunar mu...
    Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rum ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko, idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun bayyana yadda. Ummul muminina Aisha matar...
    Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shirin wanda ya ke kawo maku kissoshin da suka zo cikin Alkur’ani mai girma, ko cikin wasu littafan, wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan  na Aya. Shahida muttahari, kuma kuma cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddin Rumi. Ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirarar ImamAl-Hassan Al-Mujtaba (a) jikan manzon All..(s) kuma dan Fatimah (a) da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata mun yimaganar yakin Nahrawan, inda Imam Amirulmumina(a) ya yaki khawarijawa, wadanda su...
    144-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rum ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. ////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko , mon tsaya inda muka bayyana yadda Talha da Zubair suka bukaci Amirulmuminina (a) ya yi masu izini...
    143-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na duniyarmu a yau shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Murtadha Mutahhari ko kuma cikin littafin Mathnawa na maulana jalalluddin Rumi ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu. /////… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Alhassan Almujtaba dan Fatimah (s) diyar manzon All..(s) da muke kawo maku. A cikin shirimmu da ya gabata mun yi Magana dangane da yadda aka gudanar da hukunci tsakanin Abdullahi dan...
    142-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Shahid Aya. Muttahari, ko kuma littafin Mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu nay au. /////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata , a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan Al-Mujtaba (a) jikan manzon All..(s) kuma dan Fatima (s) da muke kawo maku a cikin shirin da ya gabata, munyi maganar yadda Khawarijiwa suka ki...
    Akwai amfani saboda watarana wani abu zai taso mai muhimmanci, iyayensa ba sa kusa za su saukaka ta hanyar kiransu. Matsalar sa lalacewar karatu, koyan dabi’un marasa kyau da masu kyau, basu ko siya musu ba laifi ba ne, amma dai a tsananta saka musu ido dan gudun baraka da lalacewa. Ya zamo kiran mai amfani ne da karatu za su rika yi da shi, ba tiktok ko Instagram ko Twitter ba. Allah ka shirya mana zuriya, ka sa mu dace. Sunana Anas Bin Malik Achilafiya, Karamar Hukumar ‘Yankwashi, Jihar Jigawa: Amfanin bayar da waya ga kananan yara; yana saukaka musu sadarwa ga iyaye, abokai, da sauran su, samun ilimi da bincike ta hanyar intanet. Iya jawo jaraba, ko dogaro...
    141- Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Shahid Aya. Muttahari, ko kuma littafin Mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu nay au. /////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata , a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan Al-Mujtaba (a) jikan manzon All..(s) kuma dan Fatima (s) da muke kawo maku a cikin shirin da ya gabata, munyi maganar yadda Aka ayyana...
    Dagacin garin Kirawa a Ƙaramar Hukumar Gwoza, a Jihar Borno, Abdulrahman Abubakar, ya bayyana dalilin da ya sa ya tsere daga Najeriya zuwa Kamaru bayan harin Boko Haram. A farkon makon nan, mayaƙan Boko Haram sun kai hari garin Kirawa, inda suka kashe mutum biyu sannan suka ƙone fadarsa. ’Yan bindiga sun sace uwa da ’ya’yanta a Kogi Isra’ila ta kai hare-hare a Gaza duk da kiran Trump na tsagaita wuta A hirar da aka yi da shi, Abubakar ya ce babu wani zaɓi da ya rage masa face ya tsere. “Babu abin da ya rage sai na tsere zuwa Kamaru. Mazauna garin sun hau manyan motoci sun tsallaka iyaka, wasu kuma sun gudu zuwa Maiduguri.” Boko Haram ta saki...
    Da farko za ki wanke tsamiya sai ki dafa ta ki tace sannan ki wanke danyar citta sai ki nika ta, sannan ki samu roba mai kyau sai ki tace tsamiya tare da cittar kisa suga da filebo sai ki juya sosai ki sa a firij ko ki sa masa kankara. Asha dadi lafiya. Hadadden Lemon Shayi: Abubuwan da uwargida za ki tanada: Kankana, kokumba, sitoru beri na ruwa, lemo, tea bag, danyar citta, abarba, Lemon juice, na’a na’a. Yadda zaki hada: Da farko za ki wanke kankana da danyar citta sai ki nika su, sannan ki tace ki zuba a cikin tukunya, sai ki dora akan wuta ki wanke abarba da kokumba, ki yanka ki zuba a cikin tukunya...
    Shugaban Amurka ya ce: Dole ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta daina kai hare-hare kan Gaza nan take domin samun damar sakin fursunoninta Shugaban Amurka Donald Donald Trump, bayan da kungiyar Hamas ta fitar da martanin kan yarjejeniyar zaman lafiya a Gaza, ya yi kira ga gwamnatin mamayar Isra’ila da ta gaggauta dakatar da kai hare-hare a zirin Gaza. Shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira ga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila a daren Juma’a da ta dakatar da harin bam da take kaiwa Gaza, yana mai cewa; “Dole ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta gaggauta dakatar da kai hare-hare a zirin Gaza domin a samu damar zakulo mutanen da aka yi garkuwa da su cikin aminci da gaggawa.” Da yake mayar da...
    Babban jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Mika fursunoni da gawarwaki cikin sa’o’i 72 ba gaskiya ba ne a halin da ake ciki yanzu. Babban jami’in kungiyar Hamas Musa Abu Marzouk ya tabbatar a ranar Juma’a cewa, batun mika fursunoni da gawarwakin yahudawan sahayoniyya cikin sa’o’i 72 lamari ne na nazari, ba tabbas ba, a halin da ake ciki yanzu.” Abu Marzouk ya bayyana cewa: Kungiyar Hamas ta amince da shirin Amurka da aka gabatar “a bisa ka’ida,” yana mai cewa “aiwatar da shi yana bukatar tattaunawa.” Ya kuma lura da cewa dukkan bayanai da suka shafi rundunar wanzar da zaman lafiya “yana bukatar fahimtar juna da fayyace shi dalla-dalla.” Dangane da batun makamai kuwa, Abu Marzouk ya bayyana a...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    ’Yan bindiga sun sace wata matar aure da ’ya’yanta biyu a yankin Bareke-Egbe a Ƙaramar Hukumar Yagba ta Yamma da ke Jihar Kogi. ’Yan bindigar sun kai farmaki gidan wani manomi mai suna Tokpe Gody da misalin karfe 2 na dare ranar Juma’a, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su sace matarsa da ’ya’yansa biyu. Rahotanni sun ce Gody ya sha da ƙyar amma ya samu raunukan harbin bindiga a jiki da ƙafafuwansa, kuma yana karɓar magani a asibitin Egbe, inda likitoci ke cewa yana cikin mummunan yanayi. Wani mazaunin yankin mai suna Samuel Adeyemi ya ce: “Tokpe Gody manomi ne mai fama da yadda zai ciyar da iyalinsa. Ya tsira da ƙyar daga ’yan bindigar, amma matarsa da ’ya’yansa...
    “Rushewar wannan gada na haifar mana da matsala sosai. Gwamnati ta taimaka ta gyara,” in ji Wayu Bamga, mazaunin yankin. Nanlong Nyas ya ƙara da cewa, “Gyaran da aka yi bai daɗe ba kafin ruwa ya sake lalata gadar.” Wasu direbobi kamar Umar Sa’adu da Abubakar Haruna sun ce duk lokacin da suka isa wurin gadar, sai sun biya ma’aikata su tura motarsu kafin su iya tsallaka rafi kana su ci gaba da tafiya. Rushewar Gadar Namne Ta Taraba Ta Tsayar Da Zirga-Zirga A Jihar Taraba kuwa, Gadar Namne dake kan hanyar Jalingo–Wukari  ta rushe a watan Agustan 2024 bayan ruwan sama mai yawa, kuma har yanzu shekara guda bayan haka, babu wani gyara da gwamnatin tarayya ko ta jiha...
    ’Yan bindigar da ke addabar yankunan karkara sun kaƙaba sun ƙaƙaba musu haraji da ke kaiwa Naira miliyan 10 a Ƙaramar Hukumar Mashegu Jihar Neja. Rahotanni sun nuna cewa an umarci al’ummomin yankunan Babban Rami da Kaboji su su biya Naira miliyan biyu-biyu. Yankin Sabon Rijiya da Sabon Rami an umarce su da su Naira dubu 500, yayin da aka umarci ƙauyukan da ke kusa da Dajin Keji su tara Naira miliyan 10 gaba ɗaya. Haka nan, ana ƙaƙaba wa al’ummar Khizi an kaƙaba musu harajin Naira miliyan shida, da wa’adin ranar Juma’a, 3 ga Oktoba, 2025. Wata mata ta banka wa kanta wuta a Bauchi Sharri Jonathan ke wa Buhari don lashe zaɓen 2027 —Garba Shehu Wani mazaunin yankin...
    Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a Kasuwar Dutse Ultra-Modern Market, inda ya cika alkawarin gwamnatinsa na samar da tsaftataccen makamashi ga ‘yan kasuwa a jihar Jigawa.   Aikin wanda Hukumar Samar da Tattalin Arzikin Kasa da Samar da ayyukan yi ta Jihar Jigawa ta gudanar, ya hada shaguna 300 da wutar lantarki daga na’urorin hasken rana da aka sanya a cikin kasuwar, inda kowane shago kuma an saka masa fanka amfani da hasken rana kyauta.   Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da kasuwar a hukumance, Malam Umar Namadi ya ce shirin zai saukaka harkokin kasuwanci, da rage kashe kudi, da kuma bunkasa ribar ‘yan kasuwa.    ...
    Nijeriya za ta zama kasa mai girma duk da kalubale — Afenifere Kungiyar Yarabawa zalla ta Afenifere, ta nuna kwarin gwiwa cewa kasar za ta kasance mai girma. Sakon wannan kwarin gwiwa ya fito ne daga kakakin kungiyar Afenifere, Kwamared Jare Ajayi, a ranar Asabar yayin da LEADERSHIP Sunday ta tuntube shi a Akure, babban birnin Jihar Ondo. Kungiyar siyasa da al’umma mafi girma ta Yoruba ta ce ta dogara da wannan kwarin gwiwa “A kan alherin Allah, albarkatun da kasar ke da su, jajircewar da gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Tinubu ke nunawa wajen tabbatar da ci gaban Nijeriya, juriya da karfin hali na mutanen kasar, da kuma jimillar kwarewar da muka samu, kuma har yanzu muna samun sa.”...
    Tsohon mai magana da yawun marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Malam Garba Shehu, ya mayar da martani kan maganar tsohon Shugaba Goodluck Jonathan da ya ce ƙungiyar Boko Haram ta taɓa naɗa Buhari a matsayin wanda zai shiga tsakanin a tattaunawarsu da Gwamnatin tarayya. A yayin taron ƙaddamar da littafin “Scars: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum” wanda tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Lucky Irabor (mai ritaya) ya rubuta, Jonathan ya bayyana cewa mayaƙan Boko Haram sun taɓa zaɓar Buhari a matsayin mai shiga tsakani domin tattaunawarsu da gwamnati. Jonathan ya ce a lokacin mulkinsa, gwamnatinsa ta kafa kwamitoci daban-daban don tattaunawa da mayaƙan Boko Haram domin samun zaman lafiya. Sai dai a martaninsa bayan labarin ya karaɗe kafofi...
    Bincike ya kuma kai ga cafke wani bangare na kungiyar karkashin jagorancin Babangida, wadanda aka gano sun hada da Isah Musa da Usman Abdullahi, wadanda suka amsa laifin karya shaguna da kuma yin fashi a yankin Rigasa. Lokacin bincike, wadanda ake zargin sun ambaci masu karbar kayan sata da suka taimaka musu wajen sayar da su. Wannan ya kai ga cafke Kabiru Sabitu, wanda aka fi sani da Baban Godiya, Abdullahi Shehu da Yusuf Saleh. Haka kuma, a ranar 10 ga Satumba, an kama wani mai suna Bello bisa zargin satar waya. Kamen nasa ya kai ga kwato wayoyi hannu 45 da kwamfutar tafi-da-gidanka, tare da kama masu karbar kayan sata nasa. A wani nasara daban, a ranar 15 ga...
    Wata mata ta zuba wa kanta man fetur sannan ta banka wa kanta wuta a Jihar Bauchi. Matar wadda mai matsakaicin shekaru ce, ta yi wannan aika-aika ne a ƙofar gidan tsohon Fira Ministan Najeriya, Marigayi Sa Abubakar Tafawa Ɓalewa. Shaidu sun ce bayan saukar matar daga wani babur mai kafa uku, riƙe da galan ɗin man fetur a hannunta, ta nemi ganin Yelwa Abubakar, ’yar Marigayi Tafawa Ɓalewa, wadda ita ce Shugabar Hukumar Kula da Yara Masu Rauni da Marayu ta Jihar Bauchi (BASOVCA). Amma da aka shaida mata cewa Hajiya Yelwa ba ta nan, sai matar ta zuba wa kanta fetur ɗin ta kuma kiyasta wa kanta ashana a babbar ƙofar shiga gidan. Duk ƙoƙarin mutanen da ke...
    Kungiyar gwagwarmayar Falasdinu ta Hamas ta amince da daftarorin zaman lafiya da shugaba Donald Trump ya gabatar, wanda ganin zai kai ga kawo karshen yakin da Isra’ila ke ci gaba da yi a Zirin. A wata sanarwa da ta fitar kungiyar “ta bukaci janyewar dukkan sojojin Isra’ila, sannan ta saki dukkan Isra’ilawan da suke tsare a hannunta, masu rai da matattu.” Kungiyar, ta kuma ce sakin zai faru “idan har an tabbatar da yanayin tsarin musayar.” Don haka, kungiyar ta ce a shirye take ta shiga tattaunawa da masu shiga tsakani domin cimma manufar. Haka zalika, Hamas ta ce ta amince da mika ragamar mulkin zirin ga wata hukumar Falasdinu mai cin gashin kanta. Duk da haka, kungiyar ta bayyana...
    Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi gargadin cewa amincewa da takunkuman da kasashen yamma suka kakaba wa Iran ba bisa ka’ida ba ya sabawa dokokin kasa da kasa, inda ya yi kira ga kasashen duniya da su bijirewa haramtattun takunkuman. Jakadan Iran a Colombo Alireza Delkhosh ya bayyana cewa, gargadin na ministan harkokin wajen kasar na kunshe ne a cikin wasikun da ya aike wa takwarorinsa na Sri Lanka da Maldives. Araghchi ya yi kira ga takwarorinsa na kasashen da su dau mataki mai tsanani kan takunkumin da Amurka da kasashen yammacin Turai suka kakaba iran, bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar a ranar 28 ga watan Satumba sake dawo da takunkuman da aka kakaba wa Iran,...
    Kasashen duniya sun fara yabawa kungiyar Hamas kan amincewa da shirin zaman lafiya na Trump. Qatar mai shiga tsakanin Isra’ila da Hamas a yakin Gaza ta yaba da matakin da kungiyar ta dauka. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Qatar Maged al-Ansari, wanda kuma ya goyi bayan kiran da Donald Trump ya yi na tsagaita bude wuta ya ce ” Qatar na maraba da sanarwar da Hamas ta yi cewa ta amince da shirin na Shugaba Trump.” A nata bangare Masar tana kallon wannan a matsayin “ci gaba mai kyau.” Kuma tana fatan a sakamakon haka, bangarorin biyu “za su himmatu wajen aiwatar da shirin Shugaba Trump da kuma kawo karshen yakin,” in ji ma’aikatar harkokin wajen kasar a shafin Facebook. Ita...
    Kasashen duniya na ci gaba da yin Allah wadai da farmakin da Isra’ila ke ci gaba da kai wa kan jiragen ruwan ‘yan fafatuka dake dauke da kayan agaji ga al’ummar Gaza. Hamas ma ta yi Allah wadai da farmakin kan Global Sumud Flotilla a iyaka da Gaza wanda ta danganta a matsayin “laifi na fashin teku da ta’addanci kan fararen hula”, tana mai kira ga “dukkan masu kare ‘yanci a duniya” da su yi Allah wadai da harin. Kungiyar Jihad Islamic ta Falasdinu ta fitar da irin wannan sanarwa, inda ta bayyana harin a matsayin ” fashin teku da kuma keta yarjejeniyar kasa da kasa da kuma na jin kai”, Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya nemi...
    An gudanar da wani samame na musamman wanda ya kai ga gano bindigar da kuma cafke wadanda ake zargin. Jami’in da ya jikkata yana karbar magani a halin yanzu.” “A Damaturu, jami’an sashen A’ na Hedkwatar ‘Yansanda sun cafke Ibrahim Alhaji Ahmadu, mai shekaru 24, bisa zargin shiga gona da dabbobi da kuma yi wa wani manomi barazana da bindiga. An kwato bindiga mai kananan harsasai daga hannunsa. Rundunar ta jaddada cewa mallaka da amfani da makamai wajen tsoratar da fararen hula babban laifi ne.” Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa, “A Potiskum, an kama Dahiru Ali, mai shekaru 19, bisa zargin lalata da wata yarinya ‘yar shekara uku. Bincike ya gano cewa wanda ake zargin ya taba aikata irin...
    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Jihar Legas zuwa Jos, babban birnin Jihar Filato, a ranar Asabar, 4 ga watan Oktoba, domin halartar jana’izar Nana Lydia Yilwatda Goshwe, mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nantewe Yilwatda Goshwe. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce Shugaban Ƙasa zai kuma gana da shugabannin coci daga Arewacin Najeriya a hedikwatar COCIN da ke Jos. Ya ƙara da cewa Tinubu zai koma Legas a ranar bayan kammala ziyarar. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu...
    Mista Fall ya jagoranci tawagar Majalisar Dinkin Duniya da ta kunshi wakilai daga UNICEF, UNESCO, UNDP, UNFPA, da mata na Majalisar Dinkin Duniya a wajen taron. Ya jaddada cewa canjin al’umma ya ta’allaka ne akan jarin dan’Adam musamman ta hanyar ilmantar da ‘ya’ya mata da karfafa wa mata.   Ya kara da cewa, “tare da gwamnati da abokan huldarmu, mun himmatu wajen kawar da duk wani cikas da ke hana yara, musamman ma masu rauni damar samun ilimi”.   Fall ya gano muhimman abubuwan da ke kawo cikas ga ilimi a Nijeriya, da suka hada da rashin tsaro, tabarbarewar tattalin arziki, sauyin yanayi, da kuma ka’idojin zamantakewa da al’adu. Ya yi kira da a kara himma wajen inganta daidaiton jinsi...
    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai tashi daga Legas zuwa Jos, Babban Birnin Jihar Filato, a ranar Asabar domin halartar jana’izar mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nantewe Yilwatda Goshwe. Zai halarci jana’izar Nana Lydia Yilwatda Goshwe, mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa. Ana fargabar mutuwar mutane a gobarar tankar mai Boko Haram ta wuce yadda mutane ke tsammani — Jonathan Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, ya ce Shugaban Ƙasa zai kuma gana da shugabannin coci daga Arewacin Najeriya a Jos. Ana sa ran Tinubu zai koma Legas a ranar bayan kammala ziyarar. A gefe guda kuma, Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato ta sanar da taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a...
    Jami’a a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci ta tarayya da ke jihar ta Edo, Imade Patricia a jawabinta a wajen gudanar da horon ta bayyana cewa, an tallafa musu ne daidai da tsarin gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, na kudurin wadata kasar da abinci, musamman ta hanyar yin noman masara. Ta ce, a nan gaba; ana kuma sa ran horar da wasu dubban manoman masarar, inda ta kara da cewa; manoman 25 da suka amfana da horon, idan sun koma yankunansu za su koyar da wasu manoman horon da suka samu. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu...
    A kan zaben 2027, Abdullahi ya ce ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar sun yarda za su goyi bayan duk wanda ya lashe zaben fid da gwani. “Dukkan ‘yan takarar shugaban kasarmu sun yarda za su goyi bayan wanda ya ci zaben fid da gwani da jam’iyyar za ta gudanar,” in ji shi. Ya kara bayyana cewa nan gaba kadan kwamitin gudanarwa na jam’iyyar zai sanar da ranakun zaben fid da gwani a Osun da Ekiti kafin zaben gwamna a kowace jiha. Wadanda suka halarci taron sun hada da shugaban jam’iyyar na kasa, Dabid Mark da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da sakataren jam’iyyar na kasa, Ogbeni Rauf da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai da tsohon gwamnan...
    Anyanwu a cikin wasikarsa ya bayyana cewa an kammala dukkan shirye-shirye wasu tsare-tsare don gudanar da taron, kuma za a gudana da shi kamar yadda aka tsara. “Muna tabbatar wa hukumar zabe cewa za mu gudanar da taron kamar yadda aka tsara tun farko ba tare da dagawa ba. “Ya kamata hukumar zabe ta yi watsi da wasikar da shugaban jam’iyyar ya tura mata tun da farko na dage toron,” ya aika wa INEC wasikar ne a ranar 26 ga Satumba ba tare da sa hannunna ba. A cewar sakataren, bai kamata INEC ta yi aiki kan wata wasikar da ba sanya hannunsa hade da na Damagum ba. Wata majiyar ta bayyana cewa abin da ke faruwa yanzu ya nuna...
    Ana fargabar mutuwar wasu mutane masu ababen hawa da wasu da ke hanya  sakamakon faɗuwar wata tankar mai da ke ɗauke da mai a ranar Juma’a ta kuma tada gobara a hanyar Abeokuta zuwa Sagamu a Jihar Ogun. An samu rahoton cewa tankar ta faɗi ne ta gefenta sannan man da ke ciki ya  zube a kan titin Abeokuta zuwa Kobape-Siun-Sagamu a  daidai  wurin musayar hanyar. Boko Haram ta wuce yadda mutane ke tsammani — Jonathan NAFDAC ta lalata magungunan jabu na N15bn a Oyo Kakakin Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa na Jihar Ogun, Babatunde Akinbiyi a cikin sanarwar da ya fitar, ya ce lamarin ya janyo tashin gobara. Ya kuma ɗaura laifin haɗarin a kan gudun wuce ƙima...
    Bisa labarin da ma’aikatar harkokin albarkatun ruwa ta kasar Sin ta bayar a kwanakin baya, ana sa ran cewa, fadin sabbin gonakin da za a shawo kan matsalar zaizayewar kasa a Sin a karshen shirin raya kasa na shekaru biyar karo na 14 ya kai muraba’in kilomita dubu 340, fadin gonakin da aka tabbatar da yanayin ruwa da kasar da ke cikinsu ya kai kashi 73 cikin dari. Wani jami’in ma’aikatar ya bayyana cewa, a yayin gudanar da shirin raya kasa na shekaru biyar karo na 14, an kiyaye kyautata yanayin zaizayewar kasa a kasar Sin, kuma an cimma burin rage fadin gonakin da suka gamu da matsalar, da kuma rage illar da ruwa da iska suka haddasa wa gonaki....
    Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce Boko Haram sun fi sojojin Najeriya makamai, lamarin da ya sa yaƙin ya zama ɗaya daga cikin manyan matsalolin tsaron ƙasar nan. Ya bayyana haka ne a Abuja lokacin ƙaddamar da littafin Scars: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum da tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya rubuta. 2027: Dalilin da ya sa Atiku bai ayyana takararsa ba — Hadimi Fashewar tukunyar gas ya haddasa gobara a jami’ar Gombe Jonathan, ya ce rikicin Boko Haram ya bambanta da sauran matsalolin da Najeriya ta fuskanta kamar na ’yan tawayen yankin Neja Delta da rikicin addini ko ƙabilanci. Ya bayyana cewa Boko Haram sun samu goyon baya daga ƙasashen waje, suna...
    Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce Boko Haram sun fi sojojin Najeriya makamai, lamarin da ya sa yaƙin ya zama ɗaya daga cikin manyan matsalolin tsaron ƙasar nan. Ya bayyana haka ne a Abuja lokacin ƙaddamar da littafin Scars: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum da tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya rubuta. 2027: Dalilin da ya sa Atiku bai ayyana takararsa ba — Hadimi Fashewar tukunyar gas ya haddasa gobara a jami’ar Gombe Jonathan, ya ce rikicin Boko Haram ya bambanta da sauran matsalolin da Najeriya ta fuskanta kamar na ’yan tawayen yankin Neja Delta da rikicin addini ko ƙabilanci. Ya bayyana cewa Boko Haram sun samu goyon baya daga ƙasashen waje, suna...
    A wani sabon hari rahotanni sun ce an kashe wani manomi ɗaya yayin da wasu ’yan bindiga suka sace wasu biyar a Tungan-Gari da ke Ƙaramar hukumar Kontagora a gundumar Neja ta Arewa a jihar Neja. Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, ’yan bindiga sun kai wa al’ummar garin hari ne da misalin ƙarfe 11 na daren ranar Alhamis inda suka yi ta harbe-harbe na tsawon sa’o’i ba tare da an ƙalubalantarsu ba. Remi Tinubu ta ƙaddamar da Asibitin Koyarwa na Tarayya a Gombe NAFDAC ta lalata magungunan jabu na N15bn a Oyo Daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su akwai mata huɗu da namiji ɗaya. “Ba mu da wani zaɓi a yanzu da ya wuce mu...
    Bayanan sun bayyana cewa; “Jimillar makarantu 228 suka ci gajiyar shirin, inda kimanin dalibai 829,423 suka nema. Ya zuwa yanzu kuma, dalibai 510,378 ne suka samu wannan tallafi na bayar da rance. “Zuwa 10 ga watan Satumba, an biya kimanin Naira 53,801,717,293.00 a matsayin kudaden makaranta na daliban, yayin kuma da aka biya Naira 45,751,360,000.00 a matsayin alawus-alawus na daliban. Idan aka tattara kudaden baki-daya, jimillarsu ta kama Naira 99,553,077,293.00,” a cewar rahoton. Duk da nasarar da aka samu a fadin kasar, shirin ya fuskanci kalubale wajen ganin an yi adalci a rabon a dukkanin shiyoyin fadin kasar guda shida da ake da su. Alkaluman da LEADERSHIP ta tattara a watan Mayun 2025, sun nuna dimbin gibin da ke tsakanin...
    Sarah Mullally ta zama sabuwar Shugabar Cocin Ingila, wato Archbishop ta Canterbury, inda ta kasance mace ta farko da za ta jagoranci Cocin Ingila inda wannan muƙamin ya samo asali tun zamanin Daular Romawa da kuma al’ummar Anglican na duniya. Sarki Charles III ya amince da naɗin Mullaly bayan kwamitin da aka dora wa alhakin nemo wanda zai maye gurbin Justin Welby, wanda ya yi murabus a farkon wannan shekarar saboda wani zargi na cin zarafi, kamar yadda gwamnatin Birtaniya ta sanar a ranar Jumma’a. Cocin Ingila ita ce ta haifi ɗarikar Anglican a duniya. Mullally, mai shekaru 63, ta zama Archbishop ta Canterbury ta 106. A cikin wata sanarwa, tsohuwar ma’aikaciyar jinya ta bayyana cewa ta fahimci “babban nauyi”...
    Uwargidan Shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar da sabon Asibitin Koyarwa na Tarayya (FMC) da aka gina a garin Kumo, Ƙaramar hukumar Akko ta Jihar Gombe An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne tare da halartar Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da kuma Ministan Kula da Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Ali Pate. NAFDAC ta lalata magungunan jabu na N15bn a Oyo Fashewar tukunyar gas ya haddasa gobara a jami’ar Gombe A jawabinta, uwargidan shugaban Ƙasar ta ce wannan asibiti na nuna sakamakon jagoranci irin na hangen nesa ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ta ce, asibitin zai ƙara inganta damar samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar Jihar Gombe da ma maƙwabtan jihohi, tare da...
    Hukumar da ke Kula da Ingancin Abinci da Magunguna a Najeriya (NAFDAC) a ranar Alhamis ta lalata magunguna da kayayyakin jabu, da wa’adin aikinsu ya ƙare da marasa inganci, da jabun magunguna da darajarsu ta kai Naira biliyan 15 a garin Ibadan na Jihar Oyo. Darakta-Janar ta Hukumar NAFDAC Farfesa Mojisola Adeyeye ce ta sanar da hakan a lokacin da aka lalata magungunan a Ibadan, babban birnin jihar. 2027: Dalilin da ya sa Atiku bai ayyana takararsa ba — Hadimi An naɗa Remi Tinubu Sarauniyar Yaƙin Akko Adeyeye wanda Daraktan bincike da tabbatar da doka na NAFDAC, Martins Iluyomade ya wakilta, ya ce hukumar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da cewa abinci, magunguna, kayan kwalliya, na’urorin likitanci, sinadarai...
    Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, har yanzu bai ayyana cewa ko zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027 ba. Yayin da wasu ’yan siyasa kamar Peter Obi da Rotimi Amaechi suka nuna sha’awar tsayawa takara, Atiku ya ce “lokaci bai yi ba” domin yanke hukunci. Isra’ila ta kame dukkan jiragen ruwan da ke koƙarin kai kayan agaji Gaza An naɗa Remi Tinubu Sarauniyar Yaƙin Akko Kwanan nan, wasu rahotanni sun bayyana cewa Atiku ya faɗa wa BBC Hausa cewa zai bai wa matashi damar tsayawa takara. Wannan ya haifar da cece-kuce a kafafen sada zumunta. Amma hadiminsa, Paul Ibe, ya ce ba a yi wa maganganun Atiku kallo na tsanaki ba, an fahimce su ba daidai ba. Ibe, ya...
    Kudubi yana tare da kwayar zarrar kowace halittar Allah, shi yake isar mata da sakon magana, wanda bai zauna da wadannan mazaje ba sai ya ji magana ce mai girma, sai ya ga kamar an maida shi Allah, ya ce mai aka bar wa Allah ragowa, abun ba haka yake ba, abun mammaki da mai fadar wannan yana da wayewar da yake ganin fina-finai na Turawa, da ya ga wannan magana kai-tsaye a sarari. Misali a kan Kudubi, Turawa suna da wani fim da suke shiryawa na Dirakula (Dracula) wani mai shan jini, abun kamar tatsuniya ce suke shiryawa, amma wani ya ce an yi fada ne da Daular Usmaniyya, wato daular Turkiya, akwai abubuwa da ya ba su tsoro...
    Gwamnaton shugaba Donal Trump na Amurka ta amince da bawa gwamnatin kasar Lebanon dalar Amurka miliyo 190 don sayan makamai da kuma wasu dalar Amurka miliyon 40 don hukumar tsaron cikin gida na kasar Lebanon saboda shirin kwance damarar kungiyar Hizbullah da ke kudancin kasar. Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto Kamfanin dillancin labaran reuters na fadar haka. Wata majiya a birnin Washington ta fadawa kamfanin dillancin labaran reuters kan cewa gwamnatin Trump ta amince da bawa hukumomin tsaro na kasar Lebanon, dalar Amurka miliyon 230 don taimaka mata wajen kwance damarar kungiyar Hizbullah wacce ta hana HKI mamayar kasar. Jami’an gwamnatin kasar Lebanon sun tabbatar da labarin. Majiyar ta kara da cewa wadan nan kudade zasu...
    Yayin da yake kira ga ‘yan kasa kan cewa, kada su karaya ko fitar da rai daga rabo, Atiku ya tunatar da ‘yan Nijeriya cewa; shekarar 2027, wata dama ce da za a iya amfani da ita wajen kawar da wannan mulki na zalunci, domin tabbatar da ganin gobenmu ta yi kyau. “Babban kyawun demokuradiyya shi ne, ‘yancin samun damar kada kuri’a, duk wadanda ake zalunta; musamman mutanenmu a halin da ake ciki yanzu, za su samu damar kawar da wannan azzalumar gwamnati a zabe mai zuwa. Babu shakka, wannan shi ne ikon da babu wani dan takara da zai iya kwacewa daga al’umma,” in ji shi. Atiku ya kara da cewa, a shekara 65; Nijeriya ta kasance kasa wadda...
    Sojin Isra’ila sun kame dukkan jerin jiragen ruwa masu dauke da kayan agaji da ke ƙoƙarin shiga Zirin Gaza, inda suka kama daruruwan masu kai agajin tare da ɗaruruwan jiragen. Bidiyon da ken una tafiyar jiragen kai tsaye ya nuna yadda sojojin Isra’ila suka kutsa cikin jirgin ƙarshe da safiyar Juma’a. Fashewar tukunyar gas ya haddasa gobara a jami’ar Gombe An naɗa Remi Tinubu Sarauniyar Yaƙin Akko Jirgin Marinette mai tutar ƙasar Poland, wanda ke da ma’aikata shida, shi ne jirgin ƙarshe daga jerin Global Sumud Flotilla, wanda a baya ya ƙunshi jirage 44, da Isra’ila ta kama. Kwamitin Ƙasa da Ƙasa na Ƙoƙarin Karya Takunkumin Gaza ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa wasu daga cikin waɗanda aka kama...
    Wasan Kalankuwa A Nijeriya, 1977 A gwamnatance a wannan kasa, an fara shirya manyan bukukuwan nuna fasahohinmu da aladunmu na-dauri, cikin Shekarar 1977 a Legas. Wanda aka fara gudanar da taron, daga 15 ga Watan Janairu, zuwa 12 ga Watan Farairun Shekarar 1977. A farkon lamari, an niyyaci ci gaba da shirya bikin na baje-kolin al’ada ne a duk Shekara, da niyyar samar da hadin-kai a tsakanin jama’ar Kasa bakidaya. Da farko an kira bikin ne da FESTAC ’77, daga baya aka koma kiransa da NAFEST (National Festibal of Arts and Culture). Saboda muhimmancin irin wadannan bukukuwa, lokacin da aka fara shirya shi a wannan kasa, an sami mahalarta taron ne daga mabanbantan kasashe har kimanin hamsin da biyar (55)....
    Wata gobara da ta tashi a daren Alhamis ta lalata wani ɓangare na ɗakin kwanan dalibai mata a Jami’ar Jihar Gombe, tare da jikkata dalibai uku. Ana zargin gobarar ta tashi ne sakamakon fashewar gas ɗin girki a wani ɓangare na ɗakin kwanan da ke cikin harabar jami’ar. Da yake tabbatar da faruwar lamarin a wata hira ta wayar tarho da wakilinmu a ranar Juma’a, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kashe Gobara ta Kasa, reshen jihar, Bashir Mu’azu, ya bayyana lamarin da cewa abin takaici ne. “Lamarin ya faru ne sakamakon fashewar gas ɗin girki. Binciken farko ya nuna cewa daliba ce ta bar girki ba tare da kulawa ba,” in ji Muazu. Sai dai ya bayyana cewa babu...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Gwamnan jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, ya kaddamar da wasu sabbin motocin alfarma masu kujeru 18 guda 50, domin inganta ayyukan zirga-zirgar jama’a na jihar.   Da yake jawabi a wajen kaddamar da bikin a Gusau, babban birnin jihar, Gwamna Lawal ya bayyana ci gaban a matsayin wani sabon babi a tarihin sufuri na Zamfara.     A cewar Gwamnan, motocin bas din suna da kayan kariya na zamani da na jin dadi, wadanda suka hada da na’urorin sanyaya waje da sauran kayyakin jin dadin matafiya.   Dokta Lawal ya bayyana cewa, da gangan aka samu jinkirin tura motocin bas din bayan isowarsu, inda ya ce gwamnati ta fara samar da tsare-tsare na sa ido da kuma bin diddigi don...
    Gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya ziyarci Oke Ode da ke karamar hukumar Ifelodun domin jajanta wa al’umma da iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu sakamakon hare-haren da masu garkuwa da mutane suka kai kwanan nan.   A cikin sanarwar gwamna AbdulRazaq ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.   Ya kuma yabawa jami’an tsaro bisa kokarin da suke yi, sannan kuma ya baiwa al’umma tabbacin dawo da zaman lafiya cikin kankanin lokaci.   Sanarwar ta kuma aike da sakon ta’aziyya da jaje ga daukacin al’ummomin da aka samu cikin wannan rikici — daga Ifelodun zuwa Irepodun, Isin, Ekiti, Edu, da Patigi.   A cewarsa ana tanadin komai don rage illar hare-haren da kuma tabbatar da kawo...
    Gwamnatin jihar Nasarawa ta ce ta ware naira biliyan biyu domin biyan kudaden tallafin karatu da alawus alawus na guraben karatu a jihar.   Gwamna Abdullahi Sule ya bayyana hakan ne a lokacin bikin kaddamar da biyan alawus-alawus na shekarar 2023/2024 da aka gudanar a Kwalejin Ilimi ta karamar hukumar Akwanga ta jihar.   Gwamnan a lokacin da yake kaddamar da shirin raba kudaden ya jaddada cewa baya ga biyan kudaden NECO, gwamnatin jihar tana biyan dalibai sama da 155 tallafin karatu na kasashen waje da sama da dalibai 30,000 a fadin kasar nan.     Shima da yake nasa jawabin, kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Dokta Danladi Jatau wanda shugaban kwamitin majalisar kan harkokin ilimi Mista Abel Yakubu Bala...
    Ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga mai martaba Sarkin Zazzau Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli a fadarsa da ke Zariya.   Da yake jawabi, shugaban gidauniyar Malala, Mista Ziouddin Yousafzai ya yaba da kyakkyawar tarba da aka yi masa tare da tawagarsa, inda ya bayyana Masarautar Zazzau a matsayin babbar abokiyar tarayya wajen ciyar da manufofin Gidauniyar gaba.   Ya yi alkawarin karfafa hadin gwiwa da cibiyoyin gargajiya domin bunkasa samun ilimi da karfafawa ‘ya’ya mata samun damar da suke da ita.   A nasa jawabin, Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya yabawa gidauniyar Malala bisa ci gaba da tallafawa wajen inganta ilimin yara mata, musamman a Arewacin Najeriya.   Sarkin ya yi...
    Hukumar ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), ofishin Kano, ta gudanar da wani taron kara wa masu yi wa kasa hidima na NYSC aiki a karkashin Hukumar Ba da Agajin Gaggawa (EMVs).   An zabo mahalarta taron ne daga kungiyoyin ci gaban al’umma (CDS) a kananan hukumomin Tarauni da Dawakin Kudu Kano.   An tsara horon don ƙarfafa ilimin membobin ƙungiyar a matsayin wakilai na gaba na rage haɗarin bala’i da amincin al’umma.   Da yake jawabi a lokacin bada horon, shugaban ayyuka na hukumar NEMA Kano reshen jihar Jigawa, Dakta Nura Abdullahi, ya bukaci jami’an tsaro da su ci gaba da jajircewa wajen ci gaba da koyo.   Mahalarta taron sun nuna haɗin kai mai ƙarfi a duk...
    Hukumar Kwastam ta Kano/Jigawa ta kama jimillar kafso guda 261,750 na Polyglycine (miligiram 300) da allunan Tramadol hydrochloride 228,700 (miligiram 225) da aka boye a cikin buhunan jumbo guda biyar.   Shugaban hukumar kwastam na yankin Kano, Dalhatu Abubakar, ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano.   Ya ce an boye magungunan ne a cikin fakiti 35 na Polyglycine da kuma allunan Tramadol 28.     Yayin da yake mika haramtattun magungunan ga wakilin hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya, Konturola Dalhatu Abubakar, ya ce abubuwan na da illa ga lafiya da suka hada da lalata gabobi, jaraba, da rashin natsuwa, musamman a tsakanin matasa.   Abubakar yayi gargadi game da illolin...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    “Muna tabbatar da inganta tsarin na PCS domin a kara tabbatar da karfafa gasa a fadin diniya a fannin na sufurin Jiragen Ruwa na NPA wanda hakan zai kuma kara samar da damar janyo masu zuba hannun jari daga waje na kai tsaye da kuma kara karfafa tattalin arzikin kasar, a nan gaba,”. A cewarsa, za mu ci gaba da kulla hadaka domin mu cimma burin da aka sanya a gaba, na kara inganta ayyukan Hukumar ta NPA. Ya ci gaba da cewa, a rabin zangon farko na shekarar 2025, ingancin da aka samar a bangarorin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun bayar da gudunmawar da ta karu, zuwa kaso 19.6 a fannin fitar da kaya waje, da ba su shafi...
    Ƴan ƙasar Congo sun fara mayar da martani kan hukuncin kisa da Babbar Kotun Sojin Ƙasar ta yankewa tsohon shugaban ƙasar Joseph Kabila ranar Talata a bayan idonsa, sakamakon samunsa da laifukan yaƙi da cin amanar ƙasa. Joseph Kabila mai shekaru 54, ya mulki jamhuriyar Demokradiyar Congo tsakanin shekarar 2001 zuwa 2019 lokacin da ya mika mulki ga shugaba Felix Tshisekedi da ya gaje shi. Baya nan cikin kotu, lokacin yanke hukucin a ranar 30 ga watan Satumbar 2025 da muke ciki, saboda yana can makwabciyarsu Rwanda inda yake zaman gudun hijirar siyasa shekaru biyu da suka gabata. Yayinda magoya bayan shugaba Tshisekedi ke yabawa matakin, wasu masana siyasa da ƴan adawa na kira da a yi taka-tsan-tsan. Jam’iyyar PPRD...
    Wani abu da ya ja hanklan mutane shi ne, irin muggan makaman da ‘yan bindigar suka hallara da su a wajen kulla yarjejeniyar, wadanda kuma babu wani mahaluki da ke da ikon kwace makaman daga hannunsu, a yayin kulla yarjejeniyar, ta jeka nayi ka. Kazalika, a cikin daya daga cikin faifan Bidiyon, an ga yadda daya daga cikin shuwagabannin ‘yan bindigar ya yi bazaranar shedawa gwamnati da sauran jami’an gwamnatin da suka halarci wajen kulla sulhun cewa, idan har gwamnati ta kuskura ta kashe ‘yan bindiga dubu goma, suma za su hallaka adadin mutane kamar hakan. Wasu ‘yan Nijeriya dai, sun yi ittifakin cewa, kasar nan, ta koma tamkar, a hanun tafin ‘yan bindigar. Kulla wannan yarjeniyra dai, ta nuna...
    Lamidon Akko da ke jihar Gombe, Alhaji Umar Muhammad Atiku, ya nada Uwargidan Shugaban Najeriya Sanata Remi Tinubu, sarautar Sarauniyar Yaki a masarautar. Basaraken dai ya karrama uwargidan shugaban ƙasar ce a ranar Alhamis a wani biki na musamman da ya gudana a fadarsa. An gudanar da zangar-zangar goyon bayan Kwamishinan ’Yan Sanda a Kano Babu wanda na cewa zan janyewa takara a 2027 — Atiku A cewar basaraken, ya ba ta sarautar ce domin yabawa da gudummawar da take bayarwa wajen kare marasa ƙarfi tare da tallafawa mata da yara a fadin ƙasar nan A yayin ziyarar kwanaki biyu da ta kai jihar Gombe, Remi Tinubu ta kuma ƙaddamar da shirin Renewed Hope Initiative Flow With Confidence, wani muhimmin shiri na...
    Ministar kula da shari’a da harkokin majalisar dokoki da hakkin mata ta kasar Sao Tome and Principe Vera Cravid ta yi kira a maida dangantakar dake tsakanin kasarta da kasar Sin a matsayin misalin hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa, domin dangantakarsu tana da tarihi mai zurfi da kuma samun ci gaba a zamanin yau. (Zainab Zhang) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Sule ya bayyana cewa, “ilimi shi ne abu mafi mahimmanci da gwamnatinsa ta fi mayar da hankali akai, hakan ne ya sa aka ware kashi 36 cikin 100 na kasafin kuɗin jihar na shekarar 2025 ga sashen ilimi”.   Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta dawo da tallafin karatu na ƙasashen waje, inda a halin yanzu take ɗaukar nauyin ɗalibai 155 da ke karatu a fannoni daban-daban a ƙasashe daban-daban na duniya.   Ya ƙara bayyana cewa, gwamnatin jihar na ɗaukar nauyin ɗaliban jinya da kuma wasu a jami’o’i daban-daban a faɗin ƙasar.   “Mun kuma biya kuɗin rajistar jarabawar kammala sakandire ta kasa (NECO) ta shekarar 2025 ga ɗalibai sama da 24,000 na makarantun sakandare na gwamnati, domin...
    Gomman matasa a Jihar Kano sun gudanar da wata zanga-zangar lumana a ranar Alhamis domin bayyana goyon baya ga Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP AI Bakori. Matasan da suka gudanar da zanga-zangar sun daga kwalaye da alluna dauke da sakonnin “A bar mana CP”, “Mutanen Kano suna bayan CP,” da “Gwamna Abba Kabir Yusuf ka kyale mana CP.” Mun kama wani mahaifi kan yunƙurin safarar ‘yarsa zuwa Iraƙi — NAPTIP Babu wanda na cewa zan janyewa takara a 2027 — Atiku Zanga-zangar na zuwa ne dai bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya caccaki  Kwamishinan ’Yan Sandan kan ƙaurace wa farerin bikin cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai a ranar Larabar da ta gabata. Yayin da yake jawabi a bikin da...
    Hukumar da ke yaƙi da safarar mutane a Nijeriya (NAPTIP) ta ce ta kama wani mahaifi yana yunƙurin safarar ‘yarsa zuwa ƙasar Iraƙi. Mai magana da yawun hukumar NAPTIP na ƙasa, Vincent Adekoye, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba. Babu wanda na cewa zan janyewa takara a 2027 — Atiku An kama masu kai wa ’yan bindiga makamai da ƙwayoyi Sanarwar ta ce mahaifin na daga cikin aƙalla mutum biyar da ake zargi da safarar mutane waɗanda aka cafke a filin jiragen saman ƙasa da ƙasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. TRT ya ruwaito Adekoye na cewa an kuɓutar da mutum 24 a yayin aikin bisa jagorancin babbar daraktar hukumar, Binta Adamu Bello wanda...
    A nasa jawabin, gwamnan ya bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya tsige CP Bakori, yana mai nuni da rashin halartar rundunar ‘yansanda daga faretin bikin a matsayin rashin mutuntawa da tsoma baki cikin siyasa.   Sai dai ga dukkan alamu, kalaman gwamnan sun janyo rashin amincewar jama’a musamman a tsakanin matasan Kano. Zanga-zangar ta ranar Alhamis ta kasance cikin kwanciyar hankali da bin doka da oda, inda masu zanga-zangar ke jaddada muradin su na CP Bakori ya ci gaba da rike mukaminsa da kuma ci gaba da aikinsa ba tare da cikas na siyasa ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku....
    Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya kori dukkan Kwamishinoni da sauran masu riƙe da muƙamai a gwamnatinsa. A cewar wata sanarwa da aka fitar a Fatakwal babban birnin jihar a yammacin Laraba ta hannun babban sakataren yaɗa labaransa, Nelson Chukwudi matakin korar ya fara aiki nan take, kuma ya biyo bayan hukuncin da kotun ƙoli da ta yanke na baya-bayan nan. Matan Sojojin da aka tsare sun nemi a yi wa mazajensu afuwa 2027: Zan iya haƙura da takara in mara wa matashi mai jini a jika baya – Atiku Gwamnan, a yayin wani zama da ya yi da hadimansa domin murnar cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai a gidan gwamnati da ke Fatakwal, ya gode wa jami’an...
    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya musanta cewa yana son ya janyewa wani takara saboda matashin ɗan takara kafin zaɓen 2027. A baya dai tsohon mataimakin shugaban Ƙasa Atiku ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar shugaban Ƙasa a 2027. An kama masu kai wa ’yan bindiga makamai da ƙwayoyi Gwamna Fubara ya kori duk Kwamishinonin jihar Atiku dai ya fice daga Jam’iyyar PDP bayan ya tsaya takarar Shugaban Ƙasa a zaɓen da ya gabata. A watan Agusta, Atiku Abubakar da wasu ’yan siyasa na adawa da suka haɗa da: tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, tsohon Gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi da tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi da dai sauransu, sun koma jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar da za su yi...
    Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun jaddada aniyarsu ta watsi da duk wata barazanar makiya tare da alwashin mayar da martani mai tsanani fiye da harin alkawarin gaskiya da ya gabata A cikin wani sako mai kakkausar murya, Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun yi gargadi ga haramtacciyar kasar Isra’ila game da aikata sabbin kura-kurai tare da jaddada cewa duk wani hari da za a kai wa Iran zai fuskanci martani mai tsauri fiye da martanin Alkawarin Gaskiya na baya. Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta dauki matakin soji da na siyasa bai daya dangane da tunkarar barazanar da take fuskanta da kuma matakin da ya biyo bayan sake maido da takunkumin da kare kan kasarta, a daidai...
    Sojojin Yemen sun kai hari kan wani jirgin ruwa da yake hulda da haramtacciyar kasar Isra’ila da makami mai linzami Dakarun sojin Yemen sun sanar da cewa, da sanyin safiyar ranar Larabar nan, sun kai hari kan jirgin (MINERVAGRACHT) da makami mai linzami a mashigin tekun Aden. Sanarwar da Rundunar Sojin Yemen ta fitar ta tabbatar da cewa: Sojojin ruwan kasar sun kai wani samame na soji kan jirgin Ruwan na (MINERVAGRACHT) saboda kamfanin ya keta dokar hana shiga tashar jiragen ruwa na Falasdinu da aka mamaye. Sanarwar ta bayyana cewa an kai harin ne a mashigin tekun Aden tare da wani makami mai linzami, wanda ya yi sanadin harbo jirgin kai tsaye tare da kama jirgin. Yanzu yana cikin...
    Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya “UNRWA” ta sanar da cewa; A kowace rana Falasdinawa guda 100 ne suke yi shahada saboda zaluncin sojojin mamayar Isra’ila Babban kwamishinan hukumar ta UNRWA Philippe Lazzarini ya bayyana cewa: A kowace rana sojojin mamayar Isra’ila suna kashe kimanin Falasdinawa 100 a zirin Gaza. Lazzarini ya ce ta hanyar dandalin X, “A takaice ana kashe mutane 100 a kowace rana a Gaza, sakamakon farmakin da sojojin mamayar Isra’ila ke kaiwa ko kuma harbe-harbe a wuraren rarraba abinci da gidauniyar agaji ta Gaza ke gudanarwa.” Ya ci gaba da cewa, “A lokaci guda kuma, wasu na mutuwa saboda yunwa ko kuma rashin kula da lafiya”. Lazzarini ya kara da cewa...
    Jami’ar Tianjin wadda aka kafa a shekarar 1895 a matsayin jami’ar Peiyang, ita ce jami’ar zamani ta farko ta kasar Sin kuma ta yi na’am tare da amsa sunanta na yanzu ne a shekarar 1951. (Abdulrazaq Yahuza Jere) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Rundunar ta kuma bayyana cewa, a ranar 30 ga watan Satumba da misalin karfe 11:15 na safe, wata tawagar rundunar ta kama wasu mutane biyu a filin tirela na Dangauro. Sanarwar ta kara da cewa, “An samu wadanda ake zargin dauke da buhu bakwai da ake zargin kayan maye ne wanda aka fi sani da ‘Akuskura.’ Ko wanne buhu na dauke da kwalabe 350, adadinsu ya kai kwalabe 2,450, wanda kudinsu ya kai ₦2,450,000.   SP Kiyawa ya kara da cewa, bisa hadin gwiwar hukumomin tsaro, “Rundunar ta mika wadanda aka cafken da kayayyakin su da darajarsu ta kai N120,000,000 ga hukumar NDLEA, ta jihar Kano, domin ci gaba da bincike.” Hakazalika, jami’an rundunar sun kama wasu fitattun...
    Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong ya bayyana a jiya Laraba cewa, kasar Sin tana matukar bayyana takaicinta da kuma nadama a kan matakin da kasar Amurka ta dauka a baya, kan daftarin kudirin kwamitin sulhun MDD da aka tsara da nufin magance matsalar jin kai a zirin Gaza. A jawabin da ya yi kan amfani da hawan kujerar na ki a wajen muhawarar babban taron Majalisar Dinkin Duniya, Fu ya ce, kasashen duniya sun dade suna yin gagarumin kira na tsagaita bude wuta da dakatar da yakin da ake yi a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin asarar rayukan fararen hula da haddasa masifar tabarbarewar jin kai, inda hakan ke dakushe lamiri da tausayin bil’adama da...
    Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta yi wata babbar nasarar kama masu baiwa ’yan bindiga makamai da kama wani fitaccen mai safarar miyagun ƙwayoyi da kuma dillalan makamai ba bisa ƙa’ida ba a wurare daban-daban a faɗin jihar. Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis,  jami’an ’yan sanda da ke aiki da sashen bayanan sirri sun kama wani matashi ɗan shekara 30 mai suna Franklin Ozo a Zariya. Gwamna Fubara ya kori duk Kwamishinonin jihar Matan Sojojin da aka tsare sun nemi a yi wa mazajensu afuwa An kama shi da ƙunshin ƙwayoyin Exol guda 500, na miliyoyin Naira. “Bincike na farko ya nuna cewa,...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Ganau sun ƙara da cewa a lokacin da aka shaida wa matar cewa Yelwa ba ta nan, sai ta koma mashigar gidan ta kwarara wa kanta man fetur tare cinna ashana wanda hakan ya janyo wuta ta tashi.   Nan take lamarin ya janyo hankalin mutanen da suke kusa da wurin inda suka yi ƙoƙarin kashe wutar amma lamarin ya ƙazanta.   Daga baya kuma aka kwasheta zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), inda daga bisani ta rasu sakamakon ƙonewar da ta yi.   An kuma ce marigayiyar ɗiyar tsohon wani alkalin kotun Shari’a a Bauchi ce, wacce ta taɓa yin aure har da ‘ya’ya.   Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil a ranar Alhamis...
    Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara ya kori dukkan Kwamishinoni da sauran masu riƙe da muƙamai a gwamnatinsa. A cewar wata sanarwa da aka fitar a Fatakwal babban birnin jihar a yammacin Laraba ta hannun babban sakataren yaɗa labaransa, Nelson Chukwudi matakin korar ya fara aiki nan take, kuma ya biyo bayan hukuncin da kotun ƙoli da ta yanke na baya-bayan nan. Matan Sojojin da aka tsare sun nemi a yi wa mazajensu afuwa 2027: Zan iya haƙura da takara in mara wa matashi mai jini a jika baya – Atiku Gwamnan, a yayin wani zama da ya yi da hadimansa domin murnar cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai a gidan gwamnati da ke Fatakwal, ya gode wa jami’an...
    Gwamnatin jihar Kogi ta bayyana matuƙar alhininta kan mummunan hatsarin kwale-kwale da ya faru a kan Kogin Neja, inda aƙalla mutum 26 suka rasa rayukansu. Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa na jihar, Kingsley Femi Fanwo ya fitar a ranar Laraba ta ce wannan mummunan lamari ya rutsa da ‘yan kasuwa da suka taso daga ƙaramar hukumar Ibaji ta jihar Kogi zuwa kasuwar Ilushi a jihar Edo. Gwamna Ahmed Usman Ododo ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma umurci hukumomin da abin ya shafa ciki har da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha da su haɗa kai da ƙananan hukumomin yankin, wajen bayar da tallafi da kuma agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa. Gwamna Ododo ya ƙara da ba da tabbacin cewa gwamnatin...
    Matan Sojoji da aka tsare bisa laifuka daban-daban a yaƙin da ake yi da ’yan Boko Haram ko Ƙungiyar ISWAP a garin Maiduguri jihar Borno, a bikin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai sun roƙi shugaba Bola Tinubu da hukumomin soja da su tausaya musu ta hanyar yi wa mazajensu afuwa. Matan da yawansu ya haura 30 tare da wasu yara ’yan ƙasa da shekara biyu da suka haɗa da ‘yan uwa da abokan arziki sun ziyarci cibiyar ’yan jarida ta Nijeriya (NUJ) da ke Maiduguri a ranar Laraba don miƙa wannan koke na su. HOTUNA: Yadda Boko Haram ta lalata Kwalejin Kagara da ke Neja 2027: Zan iya haƙura da takara in mara wa matashi mai jini a...
    Matan Sojoji da aka tsare bisa laifuka daban-daban a yaƙin da ake yi da ’yan Boko Haram ko Ƙungiyar ISWAP a garin Maiduguri jihar Borno, a bikin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai sun roƙi shugaba Bola Tinubu da hukumomin soja da su tausaya musu ta hanyar yi wa mazajensu afuwa. Matan da yawansu ya haura 30 tare da wasu yara ’yan ƙasa da shekara biyu da suka haɗa da ‘yan uwa da abokan arziki sun ziyarci cibiyar ’yan jarida ta Nijeriya (NUJ) da ke Maiduguri a ranar Laraba don miƙa wannan koke na su. HOTUNA: Yadda Boko Haram ta lalata Kwalejin Kagara da ke Neja 2027: Zan iya haƙura da takara in mara wa matashi mai jini a...
    Hukumar da ke yaƙi da safarar mutane ta Nijeriya (NAPTIP) ta ce ta kama aƙalla mutum biyar da ake zargi da safarar mutane tare da kuɓutar da mutum 24 a filin jiragen saman ƙasa da ƙasa na Nnamdi Azikiwe International Airport, da ke Abuja. Jami’in watsa labaran hukumar NAPTIP na ƙasa, Vincent Adekoye, ya bayyan a ranar Laraba cewa a cikin waɗanda aka kama akwai wani mutum da ya yi yunƙurin safarar ‘yarsa zuwa ƙasar Iraƙi. Adekoye ya ce aikin, wanda aka yi bisa bayanan sirri da aka samu, ya samu jagorancin babbar daraktar hukumar, Binta Adamu Bello. Adekoye ya ce aikin, wanda aka yi bisa bayanan sirri da aka samu, ya samu jagorancin babbar daraktar hukumar, Binta Adamu Bello....