Leadership News Hausa:
2025-11-14@00:03:56 GMT

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Published: 14th, November 2025 GMT

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi kira ga kasar Japan da ta janye kalaman baya-bayan nan da firaministar kasar ta furta, dangane da yankin Taiwan na kasar Sin, in ba haka ba, ta shirya girbar sakamakon danyen aikinta.

Lin Jian, ya yi kiran ne yayin taron ganawa da manema labarai na yau da kullum a yau Alhamis, lokacin da yake amsa tambayar da aka yi masa dangane da kalaman firaministar Japan Sanaen Takaichi, game da yankin Taiwan na kasar Sin, wadanda kuma ta ki ta janyewa.

Lin, ya ce a baya-bayan nan Takaichi ta furta kalaman tayar da husuma, dangane da yankin na Taiwan, yayin da take tsokaci a majalisar dokokin kasarta, inda ta ambata yiwuwar aiwatar da matakan soji a zirin Taiwan. Lin ya ce kalaman na firaministar Japan ba su dace ba, sun kuma yi matukar keta manufar nan ta kasar Sin daya tak a duniya, da ruhin takardun siyasa hudu, wadanda Sin da Japan suka daddale, da ma yanayin gudanar da alakar kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Jami’in ya kara da cewa, wadannan kalamai na firaministar Japan, matukar tsoka baki ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, sun kuma kalubalanci moriyar kasar, tare da keta hurumin ‘yancin kan kasar ta Sin. Don haka Sin ke matukar adawa da su, kuma ba za ta amince da hakan ba. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia November 13, 2025 Daga Birnin Sin Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana November 13, 2025 Daga Birnin Sin Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

 

Ban da wannan kuma, game da batun cewa kasashen kungiyar EU suna shirin cire na’urorin kamfanonin sadarwa na kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, kamfanonin kasar Sin suna aiwatar da ayyukansu bisa doka a nahiyar Turai na dogon lokaci, wadanda suka samar da kayayyaki da hidimomi masu inganci ga jama’ar Turai, tare da samar da muhimmiyar gudummawa wajen raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma da samar da ayyukan yi a nahiyar. Kasar Sin ta kalubalanci kungiyar EU da ta samar da yanayin gudanar da ciniki cikin adalci da rashin nuna bambanci ga kamfanonin kasar Sin don magance wargaza amannar da kamfanonin suka yi wa nahiyar Turai kan zuba jari. (Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa November 11, 2025 Daga Birnin Sin CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya November 11, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15 November 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
  • Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo
  • Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin
  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
  • Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo