NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Published: 15th, November 2025 GMT
Ya kara da cewa yayin gudanar da aikin, jami’an hukumar sun gano babura hudu daga hannun wanda ake zargi babura uku na Jincheng da daya na Lifan Kumata, inda ya ce ana ci gaba da neman sauran abokan aikinsa biyu da suka tsere.
Haka kuma, ya bayyana cewa an kama mai safarar miyagun kwayoyi mai suna Salisu Abdullahi, dan shekara 28, mazaunin Semegu a Karamar Hukumar Kumbotso, a yankin Sabon Titin Dorayi, tare da tarin miyagun kwayoyi da ake zargin yana sayarwa don amfani na haram.
Kwayoyin da aka samo daga hannunsa sun hada da kwayoyi 100 na Padol 5mg, kwayoyi 30 na Pregabalin 300mg, kwayoyi 170 na Diazepam 10mg, da kuma kwaya guda daya ta karin karfin maza.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan kamun na cikin dabarun hukumar wajen rushe kungiyoyin masu aikata laifuka da ke da hannu a satar kayayyaki, lalata dukiyoyin jama’a da sauran miyagun ayyuka da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.”
Abdullahi ya ce ana ci gaba da bincike a kan wadanda ake zargi, kuma za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala binciken.
A ranar 6 ga Nuwamba, jaridar The PUNCH ta ruwaito cewa hukumar NSCDC ta Jihar Kwara ta kama mutane biyar bisa zargin satar igiyoyin wutar lantarki na transifoma da na fitilun titi a yankin Tanke da ke Ilorin.
Wadanda aka kama sun hada da Samson Akintola, Muhammed Zakariya, Mohammed Monsur, Ibrahim Hamida, da Kabir Abubakar.
An kama su ne da misalin karfe 1 na safe a ranar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025, yayin hadin gwiwar aikin jami’an NSCDC daga sashen Tanke Dibision da kuma Kungiyar Tsaro ta Bijilante ta al’ummar Tanke.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yan Najeriya 3 a Kenya kan zargin aikata damfara
An kama ’yan Najeriya uku a rukunin gidaje na Mwaliko da ke garin Mwea a ƙasar Kenya, bisa zargin su da damfara ta intanet.
Rahoton da wata kafar labarai a Kenya mai suna Tuko News ta fitar ya ce Hukumar Binciken Laifuka ta ƙasar (DCI) ce ta kama waɗanda ake zargin a ranar Laraba.
Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030 Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin JodanWaɗanda aka kama sun haɗa da Peter Chukwujekwu, Alazor Chukulute Sunday, da Nnalue Chiagozie Samwe.
A cewar rahoton da aka fitar a ranar Alhamis, an kama su a gidansu bayan jama’a sun kai ƙorafi kan take-takensu musamman da daddare a cikin ginin.
DCI ta tabbatar da kama su, tana mai cewa an gudanar da “farmakin haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da dama domin kama wata ƙungiyar masu damfara ta intanet” a yankin.
Rahoton ya ambato DCI tana cewa: “An kama ’yan Najeriya uku a wani farmakin haɗin gwiwa a Kirinyaga. Wannan farmaki da aka tsara sosai a rukunin gidaje na Mwaliko cikin garin Mwea ya tona asirin wata ƙungiyar masu damfara ta intanet da ’yan Najeriya uku ke gudanarwa.”
Waɗanda ake zargin sun ce suna gudanar da kasuwanci ta yanar gizo, amma rahoton ya nuna cewa suna zaune a Kenya ba tare da izini ba, kuma ba su da takardun aiki na doka.
Kamun nasu dai na cikin jerin kame-kamen da ake yi wa ’yan Najeriya a ƙasashen waje kan laifuka daban-daban, ciki har da damfara ta intanet, safarar miyagun ƙwayoyi, da safarar mutane.
Ko a watan Yunin 2023, sai da ’yan sandan a kasar ta Kenya suka kama ’yan Najeriya 19 a Nairobi, babban birnin kasar, bisa zargin damfara ta intanet da ke kai hari ga ’yan ƙasar.
A cewar DCI, mutanen da shekarunsu ke tsakanin 19 da 33, sun yi amfani da kafafen sada zumunta wajen fara damfarar, suna yaudarar ’yan Kenya da sunan za su tura musu kaya daga ƙasashen waje.