Aminiya:
2025-11-24@14:59:28 GMT

Jarumin fina-finan Indiya Dharmendra ya rasu

Published: 24th, November 2025 GMT

Fitaccen jarumin masana’antar fina-finan Indiya ta Bollywood, Dharmendra Deol da aka fi sani da Dharam Ji, ya mutu yau Litinin yana da shekaru 89 a duniya.

Dharam ya riga mu gidan gaskiya ne kwanaki gabani cika shekaru 90 bayan fama da doguwar jinya mai alaƙa da numfashi kamar yadda kafofin labarai suka ruwaito.

Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

A watan Nuwambar nan ne labaran ƙanzan kurege suka riƙa yaɗuwa cewa jarumin ya mutu a daidai lokacin da ake jinyar sa a asibitin Breach Candy da ke birnin Mumbai na ƙasar ta Indiya.

Bayanai sun ce tun dai cikin watan Oktoban da ya gabata, aka kwantar da Dharmendra a asibitin Candy Hospital da ke birnin Mumbai gabanin sallamar shi ranar 12 ga watan nan, sai da kuma ya koma ga mahaliccinsa da safiyar yau Litinin.

Firaiministan Indiya, Narendra Modi ya bayyana alhininsa ga rashin jarumin wanda ya bayyana da “ƙarshen shekarun fina-finan Indiya.”

Dharmendra wanda ya haska a fina-finai fiye da 300, ya shafe aƙalla shekaru 60 a masana’antar Bollywood, kodayake an fi ganin shahararsa a fina finai irin Sholay da Phool Aur Patthar baya ga Satyakam da Chupke Chupke sai kuma Dharam Veer da Anupama.

BBC ya ruwaito cewa, Dharmendra ya fara fim ne tun zamanin fina-finai marasa launi, ma’ana tun zamanin hoton bidiyo fari da baƙi, inda a shekarar 1960,  ya fito a matsayin mataimakin jarumi, wato ‘supporting actor’ a fim ɗin Dil Bhi Tera Hum Bhi Tere.

Dharmendra ya auri matarsa ta farko Parkash Kaur a shekarar 1954 suka kuma haifi ’ya’ya huɗu da suka ƙunshi Sunny Deol da Bobby Deol da Vijeta Deol sai kuma Ajeeta Deol.

A shekarar 1979 ne Dharmendra ya auri matarsa ta biyu kuma fitacciyar jaruma, Hema Malini inda suka haifi yara biyu da suka ƙunshi Esha Deol da Ahana Deol.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bollywood Dharmendra Deol Dharmendra ya

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN

Yawan ɗaliban da aka sace a makarantar Sakandaren St. Mary’s da ke Jihar Neja ya kai 215 da kuma ma’aikata 12 a cewar Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN).

Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Reshen Jihar Neja, Rabaran Bulus Dauwa Yohanna, ya ce mutum 227 aka sace a makarantar, ɗalibai 215 da kuma malamai 15.

A safiyar Juma’a ne ’yan bindiga suka kutsa makarantar da ke yankin Papiri da ke Karamar Hukumar Agwara ta jihar Neja suka yi awon gaba da su.

Da yake jawabi bayan ziyartar makarantar, ya bayyana cewa, “Na gana da iyayen ɗaliban kuma mun tabbatar musu cewa muna aiki tare da gwamnati da jami’an tsaro domin ganin an ceto yaran.

Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya

“Alƙaluman da aka tattara sun nuna yara 215 da malamai 12 ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a garin.

“Akwai yaran da suka tsere a lokacin da aka kai harin, kuma iyayen sun zo suka kwashe ’ya’yansu tunda an rufe makarantu,” in ji shi.

Aminiya ba ta iya tabbatar da alƙaluman ba, kuma hukumomi ba su fitar da nasu alƙaluman ba, zuwa lokacin da muka kammala wannan labari.

Wakilinmu ya gano cewa da misalin ƙarfe 2 na dare ne ’yan bindigar suka kai harin, inda daga bisani suka loda ɗaliban da malaman a cikin wata babbar mota da suka ƙwace a yankin.

Daga baya sun jefar da motar a hanya bayan da ya samu matsala, suka kora mutanen zuwa cikin daji.

An kai harin ne kwana huɗu bayan a ranar Litinin ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai 26 makarantar ’yan mata ta GGCSS da ke yankin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu da ke Jihar Neja — ’yan bindigar na neman kuɗin fansa Naira miliyan 100 a kan ɗaliban.

Aminiya ta ruwaito cewar Gwamnatin Tarayya ta ba da umarnin rufe duk makarantunta na kwana guda 41 da ke faɗin ƙasar nan a sakamakon hare-haren.

Kafin nan gwamnatin jihar Katsina ya rufe ɗauƙacin makarantu, gwamnatin Filato ta rufe ɗauƙacin makarantun ƙananan sakandare, a yayin da gwamnatin Kwara ta rufe wasu makarantu 50 a wasu yankuna saboda tsaro, bayan sace Ɗaliban Makarantar Maga.

Gwamnatin Jihar Neja zargi Hukumomin Makarantar St. da rashin bin umarnin kada a bisa ga makarantar saboda rashin tsaro a yankin, amma hukumomin makarantar suka yi biris da umarnin gwamnatin suka yi gaban kansu wajen buɗe makarantar, lamarin da ya jefa rayuwar dalibai da malaman cikin haɗari.

Idan ba a manta ba, bayan harin Makarantar Maga, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Ministan Tsaro Bello Matawalle da ya koma Jihar Kebbi, jami’an tsaro kuma su tabbata sun ceto yaran cikin aminci.

SP Wasiu Abiodun, kakakin ’yan sanda na Jihar Neja, ya tabbatar da harin tare da cewa an tura jami’an tsaron haɗin gwiwa na musamman domin ceto ɗaliban da malamansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • An rufe duk makarantu a Kebbi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 160
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN
  • Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar