Aminiya:
2025-11-23@12:09:21 GMT

An rufe duk makarantu a Kebbi

Published: 23rd, November 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kebbi ta ba da umarnin rufe dukkan makarantun sakandire na gwamnati da na masu zaman kansu nan take.

Haka kuma, gwamnatin ta rufe dukkan manyan makarantun gaba da sakandire a faɗin jihar, banda Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi.

An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 

Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi na manyan makarantu, Alhaji Issa Abubakar-Tunga, tare da Kwamishiyar Ilimin Firamare da Sakandare, Dokta Halima Bande, suka fitar a Birnin Kebbi, ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne sakamakon barazanar hare-haren da ake samu a wasu sassan jihar a kwanakin nan.

Manyan makarantu da abin ya shafa sun haɗa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Dakingari, Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kebbi (KSUSTA) da ke Aliero, Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jega, da kuma Kwalejin Ilimi ta Argungu.

Sanarwar ta ce Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi ba ta cikin jerin makarantun da aka rufe.

Gwamnati ta buƙaci hukumomin dukkan makarantun da su yi wa wannan umarni biyayya, tare da kwantar da hankalin al’umma, tana mai bayyana cewa nan gaba kaɗan za a ayyana ranar komawa makarantun da zarar komai ya daidaita.

Aminiya ta ruwaito yadda a bayan nan jihohi da dama musamman a Arewacin suka bayar da umarnin rufe makarantu saboda fargabar matsalar tsaro da ake ci gaba da samu a kwanakin nan.

Wasu daga cikin jihohin da suka rufe makarantu sun haɗa da Kwara, Neja, Katsina, Taraba, Yobe da kuma Filato.

Wannan dai na zuwa ne bayan ’yan bindiga sun sace ɗalibai 25 a wata Makarantar Sakandire ta Maga da ke Jihar Kebbi.

Sai kuma harin da aka samu a wani coci da ke Jihar Kwara da kuma sace fiye da ɗalibai 300 da ’yan ta’adda suka yi a wata makarantar St Mary da ke Jihar Neja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta tabbatar da bada cikakken goyon bayanta ga Kwalejin Aikin Noma ta Gwamnatin Tarayya da ke Kirikasamma.

Gwamna Umar Namadi ya bayar da wannan tabbaci ne lokacin da ya karɓi tawagar gudanarwar kwalejin ta farko, ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Dr. Muhammad Yusha’u Gwaram, yayin ziyarar girmamawa da suka kai Gidan Gwamnati da ke Dutse.

Ya taya shugaban kwalejin da tawagarsa murna, inda ya bayyana nadin nasu a matsayin tarihi kuma mai matuƙar muhimmanci.

Malam Umar Namadi ya ƙara da cewa kafa sabuwar cibiyar ilimi aiki ne babba, yana mai bayyana tabbacin cewa  mutanen da aka zaba don fara gudanar da kwalejin za su taka rawar gani.

“Kafa sabuwar cibiyar ilimi ba abu ba ne mai sauƙi. Kun shiga tarihin wannan kwaleji, wacce idan ta yi nasara, za a tuna da ku cikin alheri; idan ta gaza kuma, babu shakka hakan zai shafe ku. Amma ina da tabbaci, ganin irin mutanen da ke cikin wannan tawaga, cewa kwalejin ta fara da ƙafar dama,” in ji shi.

Namadi ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da dokokin da suka kafa Kwalejin Noma ta Tarayya a Kirikasamma da Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Birnin Kudu, inda ya bayyana cewa Jigawa na kan hanyar samun wata cibiyar tarayya ta uku bayan tattaunawar da ya yi da shugaban ƙasan.

Gwamna Namadi ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da cikakken goyon baya ga tawagar gudanarwar.

 

“Za mu yi duk mai yiwuwa don tabbatar da nasarar fara aiki a kwalejin, kuna da cikakken goyon bayanmu, mun yi sa’a sosai da samun Dr. Gwaram a matsayin jagoran wannan cibiyar, ƙwararren masani a fannin noma, gogaggen mai gudanarwa, kuma ɗan asalin Jigawa mai kishin ƙasa.”

Ya yaba wa Ministan Noma, Ministan Ilimi, da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Mazabar Birniwa/Guri/Kirikasamma, Alhaji Fulata, kan rawar da suka taka wajen ganin an kafa sabuwar kwalejin.

Haka kuma ya jinjinawa shugaban kwalejin da Kwamishinan Ilimi na manyan makarantu bisa jajircewarsu.

Tunda farko, shugaban kwalejin, Dr. Muhammad Yusha’u Gwaram, ya bayyana godiyarsa ga gwamnatin jihar bisa goyon bayanta, tare da jaddada cewa kwalejin ta shirya fara aiki nan take.

A cewarsa, kwalejin za ta kasance cibiya ta musamman da za a koyar da ingantattun hanyoyin noma na zamani.

Ya bayyana cewa sun shirya horas da manoma da kuma jawo hukumomin da suka dace zuwa Jihar Jigawa.

Ya ce sun fara tattaunawa da hukumomin da ke da alhakin rajista da tsari kamar NBTE da sauran da ake buƙata don fara aiki.

Ya yaba da irin  ƙoƙarin da aka yi wanda ya kai ga amincewa da kafa cibiyar, yana mai jaddada yawan tattaunawar da aka yi da hukumomin tarayya, masu tsara doka, da masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar wa gwamna cewa tawagarsu za ta yi aiki tukuru wajen cimma nasara kwalejin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Ba da Umarnin Rufe Makarantu 41 Nan Take
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN
  • Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro