NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Published: 13th, November 2025 GMT
NDLEA ta bayyana cewa za ta ci gaba da jajircewa wajen yaƙar wannan matsala, tare da wayar da kan jama’a da kula da masu fama da shan ƙwayoyi, domin kare tsaron rayuka da zaman lafiya a ƙasar nan.
Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai wakilin shugaban NDLEA, Birgediya Janar Muhammadu Buba Marwa (mai ritaya), wato Kwamanda Muhammadu Tukur; wakilin Gwamnan Jihar Kaduna, da wakilin Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, wato Alhaji Umar Muhammad Fagacin Zazzau.
Haka kuma, Kwamandan NDLEA na Jihar Kaduna da wakilai daga ‘yansanda, sojoji, DSS, da sauran hukumomin tsaro sun halarta.
Masu jawabi a wajen taron sun nuna farin ciki da wannan nasara, tare da yabawa jami’an tsaro, alƙalai, da jama’ar gari bisa gudunmawar da suka bayar.
An kammala taron lafiya, kuma kowa ya watse lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
Daga Aliyu Lawal
Karamar Hukumar Agwara da ke Jihar Neja ta ce za ta ci gaba da hada kai da Gwamnatin Tarayya ta Jiha Neja wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’arta, musamman masu rauni.
Shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Iliyasu Zakari, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya rattaba hannu da kansa, wadda ya rabawa manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.
Alhaji Iliyasu Zakari, wanda ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne ginshikin mulkinsa, ya kuma yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro (NSA) Nuhu Ribadu, hukumomin tsaro da Gwamna Mohammed Umar Bago bisa rawar da suka taka wajen tabbatar da sakin dalibai ɗari da aka sace a makarantar Cocin Saint Mary’s Catholic da ke Papiri.
Alhaji Iliyasu Zakari ya ce: “Muna matuƙar godiya ga Shugaba Tinubu, Gwamna Umar Bago, Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, da jaruman jami’an tsaro bisa jajircewarsu wajen kare lafiyar ’ya’yanmu.”
Shugaban ya kuma yi kira da a ci gaba da yin addu’a da bayar da goyon baya ga hukumomi domin tabbatar da dawowar sauran ɗalibai da malamai da har yanzu ba a same su ba, yana mai cewa: “Muna da yakinin cewa, da irin wannan haɗin kai da kula da tsaro, sauran yara da malamansu za su dawo cikin iyalansu ba da jimawa ba.”
Sai dai Alhaji Iliyasu Zakari ya yi kira ga iyaye, al’ummar Neja da ’yan Najeriya gaba ɗaya da su kwantar da hankalinsu domin Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Neja na aiki tare da hukumomin tsaro wajen tabbatar da sakin sauran ɗalibai da malamai da ke tsare a hannun masu garkuwa da mutane.