Aminiya:
2025-12-13@12:59:38 GMT

Mutfwang ya musanta raɗe-raɗin sauya sheƙa zuwa YPP

Published: 14th, November 2025 GMT

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya ƙaryata jita-jitar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa YPP.

Rahotanni na yawo a shafukan sada zumunta cewa ya sauya sheƙa, amma mai magana da yawunsa, Gyang Bere, ya ce labarin ƙarya ne, tare da buƙatar jama’a su yi watsi da shi.

Ɗalibar BUK ta samu kyautar motar N35m a gasar MTN Cin ganda na sa Najeriya tafka asarar $5bn — Gwamnatin Tarayya

Bere, ya ce labarin ƙarya ne aka shirya domin haifar da rikici.

“Wannan zancen ƙarya ne da wasu ke yaɗawa domin su rikita al’umma,” in ji shi.

Ya bayyana cewa gwamnan yana nan daram a jam’iyyar PDP, kuma yana mayar da hankali kan ci gaban al’ummar jihar.

A baya-bayan nan, APC ta yi iƙirarin cewa gwamnan na ƙoƙarin sauya sheƙa zuwa cikinta, amma Mutfwang, ya ce ba shi da niyyar sauya sheka, duk da matsin lambar da yake fuskanta daga wasu.

Sai dai majiyoyi daga PDP sun ce gwamnan na iya komawa wata jam’iyyar a nan gaba, idan rikicin jam’iyyar ya ƙi ƙarewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Mutfwang Sauya Sheƙa Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno

Dakarun Sojin Rundunar Operation Haɗin Kai, sun kashe ’yan ta’adda biyu a wani samame da suka kai yankin Shettimari da ke Ƙaramar Hukumar Konduga, a Jihar Borno.

Majiyoyi sun shaida cewa rundunar ta kai harin ne ƙarƙashin Operation Desert Sanity V da safiyar ranar Alhamis.

Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai

Wata majiyar soji ta ce, “Sojojin sun tare mayaƙan a kusa da inda suka ke shirin kai hari a yankin da misalin ƙarfe 1:20 na dare.”

Ya ƙara da cewa, “Sojojin sun yi nasarar daƙile ’yan ta’addan nan take, inda suka kashe biyu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere.”

Bugu da ƙari, majiyar ta ce daga baya an gano wasu bama-bamai guda biyu da kuma wani gidan harsashi guda ɗaya mai ɗauke da harsasai 23 masu ɗangon 7.62mm x 39mm da ’yan ta’addan suka watsar yayin tserewa.

Majiyar ta ƙara da cewa, “Babu wanda ya mutu a cikin sojojin, sai dai daga baya tawagar sojojin sun ci gaba da aikinsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky