Aminiya:
2025-11-23@08:26:47 GMT

Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 

Published: 23rd, November 2025 GMT

Ƙungiyar Ƙwadago ta Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa (NUEE) ta yi barazanar dakatar da dukkan ayyukan samar da wutar lantarki a faɗin Najeriya, sakamakon harin da ta ce jami’anta sun fuskanta a Jihar Imo.

Ƙungiyar ta bayyana cewa wasu jami’an ’yan sanda ɗauke da makamai ne suka kai wa ma’aikatanta hari a Egbu 132/33kB Transmission Substation da ke Owerri, Jihar Imo, lamarin da ya janyo fargaba da tayar da hankali ga ma’aikatan da ke wurin.

Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na ƙasa ya fitar, NUEE ta ce wannan hari na nuna take haƙƙin ma’aikaci, kuma ba za a lamunta da shi ba.

NUEE ta bayyana cewa ba za ta yi shiru ba yayin da tsaro da mutuncin mambobinta ke fuskantar barazana ba.

Sanarwar ta ce, “Wannan hari da jami’an tsaro suka kai ya saɓa wa duk ka’idojin aikin yi. Jami’anmu na gudanar da aikinsu ne na yau da kullum, amma aka afka musu da duka da barazana. Mun gaji da irin wannan cin zarafi.”

Ƙungiyar ta gargaɗi gwamnati da shugabannin rundunar ’yan sanda da cewa za ta rufe dukkan tashoshin wutar lantarki a sassan ƙasar, muddin ba a ɗauki matakin hukunta masu laifin da kuma bada tabbacin tsaron ma’aikata ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja

Rundunar ƴansandan jihar Neja ta ce tuni ta aika jami’ai yankin da aka sace wasu ɗalibai da ba a san adadin su ba har yanzu domin kuɓutar da su.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP W. A Abiodun ya fitar, ya ce an aika jami’an tsaro da haɗin gwiwar sojoji da sauran jami’an tsaro zuwa yankin da lamarin ya faru.

Sanarwar ta ambato kwamishinan ƴansandan jihar, CP Adamu Abdullahi Elleman na jaddada ƙudirin rundunar na kuɓutar da ɗaliban ba tare da ji musu ciwo ba.

Kwamishinan ƴansandan ya kuma yi kira ga al’umma su kwantar da hankali tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai a ƙoƙarin da suke yi na kuɓutar da ɗaliban.

Ya kuma ce daga bisani za a ɗauki mataki kan hukumomin makarantar saboda ci gaba da karatu bayan umurnin kulle makarantu a yankin saboda barazanar tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daliban Jami’ar st Gorges Ta Birnin London Sun yi Zanga-zangar Nuna Adawa Da Daukar Tsohon Sojan Isra’ila Aiki
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai