Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
Published: 14th, November 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta umarci Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Shirya Jarabawar Afrika ta Yamma (WAEC) da su dakatar da shirin fara amfani da tsarin jarabawa ta kwamfuta a jarabawar kammala sakandare ta shekarar 2026.
Umarnin ya biyo bayan amincewa da wani kudiri na gaggawa da Kelechi Wogu ya gabatar a zaman majalisar na ranar Alhamis.
Kudirin na Wogu mai taken: “Bukatar Daukar Mataki Don Kaucewa Yawan Faduwa a Jarabawar Kwamfuta da WAEC ke Shirin Gudanarwa a 2026,” ya yi gargadin cewa gaggauta amfani da tsarin na iya haifar da yawan faduwa da kuma jefa dalibai cikin damuwa.
Wogu ya nuna damuwa kan yadda Ma’aikatar Ilimi ke da niyyar ci gaba da tsarin jarabawa ta kwamfuta duk da adawar da ke fitowa daga Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa da shugabannin makarantu, musamman a yankunan karkara inda fiye da kaso 70 cikin 100 na masu jarabawar ke zaune.
Ya ce yawancin makarantu, musamman a yankunan karkara, ba su da dakunan kwamfuta masu aiki, babu intanet, babu wutar ingantacciyar lantarki, kuma ba su da malamai masu ƙwarewa a fannin fasahar zamani.
Ya jaddada cewa fara amfani da tsarin a irin wannan yanayi zai zo da matsala, yana ambato matsalolin fasaha da suka shafi shafin sakamakon WAEC na 2025 a matsayin shaidar rashin shiri.
Domin magance waɗannan ƙalubale, Majalisar ta umarci Ma’aikatar Ilimi da ta haɗa kai da gwamnatocin jihohi domin saka ayyukan daukar malamai masu koyar da kwamfuta, gina dakunanta, samar da kayan intanet da kuma wutar lantarki a cikin kasafin kuɗin shekarar 2026 zuwa 2029.
Majalisar ta kuma yanke shawarar cewa kada a fara amfani da tsarin jarabawar kafin shekarar karatu ta 2030.
Majalisar ta amince da kudirin gaba ɗaya, tare da umartar kwamitocinta kan Ilimi a matakin farko, Fasahar Zamani da Bayani, Hukumomin Jarabawa, da Ma’aikata da su tattauna da masu ruwa da tsaki sannan su gabatar da rahoto cikin makonni huɗu domin ɗaukar matakin dokoki na gaba.
An kirkiro da tsarin jarabawa da kwamfuta ne a Najeriya ne domin rage yawan magudin jarabawa da kuma sabunta tsarin ilimi na ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai WAEC da tsarin jarabawa amfani da tsarin
এছাড়াও পড়ুন:
An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa
Hukumar Kula da jin dadin mahajjan Jihar Taraba ta bayyana 1 ga Disamba, 2025, a matsayin ranar ƙarshe ga masu niyyar yin hajji don kammala biyan kuɗin tafiyar hajji ta shekarar 2026.
A cewar wata sanarwa da Sashen Bayani na Hukumar ya fitar ta bakin Mataimakin Daraktan Hamza Baba Muri, an ƙayyade sabon kuɗin hajjin 2026 a Naira miliyan 7,630,000, kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta amince.
Hukumar ta yi kira ga duk masu shirin yin hajji ta wannan tsari su tabbata sun biya kuɗin gaba ɗaya kafin ƙarshen wa’adin domin samun tabbacin shiga cikin masu sauke farali shekara mai zuwa.
Mai magana da yawun Hukumar ya jaddada cewa dukkan biyan kuɗi dole ne a yi su ta hannun Jami’an Cibiyoyin da aka keɓe, yana mai gargadin cewa ba za a karɓi korafi ba bayan wa’adin ƙarshe.
Ya bayyana cewa biyan kuɗi a kan lokaci zai bai wa Hukumar damar tattara jerin sunayen fasinjojin ƙarshe da kuma tura kuɗaɗen zuwa NAHCON bisa jadawalin ƙasa.
Haka kuma, mai magana da yawun Hukumar ya ce ana ci gaba da tattaunawa da masu samar da ayyuka a Saudi Arabia domin tabbatar da abinci mai inganci da wuraren kwana ga fasinjoji a Makkah yayin hajjin 2026.
Hukumar ta sake jaddada kudirinta na samar da mafi kyawun ayyuka ga fasinjojin Taraba, bisa manufa da burin Gwamnatin K-move.
END/JAMILA ABBA