Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
Published: 14th, November 2025 GMT
Babban taron dandalin kafafen yada labarai na kasashe masu tasowa da kwararru na kawancen Sin da Afirka da aka bude a jiya Alhamis a birnin Johannesburg da ke kasar Afirka ta Kudu, zai lalubo hanyoyin karfafa hadin gwiwa, da fadada yin magana da murya daya a tsakanin kasashe masu tasowa da kuma habaka gudanar da tsarin shugabancin duniya na bai-daya.
Wanda kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da Tarayyar Afirka (AU) da kamfanin Independent Media na kasar Afirka ta Kudu da sauran abokan hulda suka shirya, taron na kwanaki biyu ya samu halartar wakilai sama da 200 daga kafofin watsa labarai fiye da 160, da kungiyoyin kwararru, da hukumomin gwamnati da sauran cibiyoyi daga kasar Sin da kasashen Afirka 41, da kuma kungiyar AU.
A karkashin taken “garambawul ga tsarin shugabancin duniya: sabbin rawar da za a taka da kudurori na hangen nesa ga hadin gwiwar Sin da Afirka,” taron ya mayar da hankali ne kan yadda hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai da kungiyoyin kwararru zai iya ba da gudummawa wajen tsara shugabanci na duniya mafi adalci da ya hade kowa da kowa.
ADVERTISEMENTTaron ya kuma kunshi fitar da wani rahoto na kwararru mai taken “gina sabon tsarin shugabancin duniya–yin aiki tare don neman samar da tsarin shugabancin duniya mai adalci da ma’ana,” da kuma kaddamar da turbar sadarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa mai lakabin “hadin kai a cikin zukata, hanya da kuma aiki–shirin aiki kan karfafa hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2026.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: tsarin shugabancin duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda muka daƙile yunƙurin tsige Akpabio daga shugabancin Majalisa – Orji Kalu
Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana yadda wasu ’yan majalisa suka haɗa kai suka daƙile yunkurin tsige Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio.
Yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Talata a Majalisar Tarayya da ke Abuja, Sanata Kalu ya tabbatar da cewa akwai yunkuri daga wasu ’yan majalisa na tsige Akpabio daga mukaminsa, wanda bai yi nasara ba.
Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a YobeKalu wanda kuma tsohon Gwamnan Jihar Abia ne ya ce, “Kodayake an yi yunkuri, amma ba mu bari hakan ta faru ba. Shi ya sa kullum nake cewa mu ’yan gida daya ne, kuma hakan ba zai faru ba,” in ji shi.
Ya jaddada cewa Majalisar Dattawa na da hadin kai kuma tana mayar da hankali kan aikinta na doka, musamman wajen tallafa wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin fuskantar kalubalen tattalin arziki da ’yan Najeriya ke fuskanta.
‘Soludo zai iya komawa APC’
Dangane da ci gaban siyasa a Kudu Maso Gabas, Kalu ya nuna yiwuwar Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, zai sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
A yayin da yake amsa tambaya kan makomar siyasar Soludo, Kalu ya ce: “Ina ganin bayan shari’o’in da ke gabansa, Soludo mutum ne mai ra’ayin cigaba kamar ni, Shugaba Tinubu, da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da kuma gwamnonin APC na Imo, Ebonyi, Enugu da sauransu. Don haka Soludo mutum ne mai ra’ayin ci gaba.”
“Ba na ganin wani abu ne da ba daidai ba idan ya shigo APC. A gaskiya, an tabbatar da cewa zai shiga jam’iyyar. Babu wani zabi da ya fi dacewa da shi face ya zo mu hada kai.”
Kalu ya kuma bayar da tabbacin cewa Shugaba Tinubu zai samu wa’adi na biyu, yana mai cewa a halin yanzu babu wata gagarumar adawa da ke kalubalantar shi.
“Shin akwai wani da ke fafatawa da shi? Zaben nan Tinubu ne da Tinubu, kamar yadda Soludo ya fafata da kansa a zaben Abia.”
“Shugaban kasa ba shi da adawa. Jam’iyyarmu tana da karfi a kasa kuma muna tare da jama’a. Babu wanda zai ce ba mu da jama’a. Za mu ci gaba da yin iya kokarinmu domin ganin talakawan Najeriya sun samu ci gaba,” in ji shi.