Babban taron dandalin kafafen yada labarai na kasashe masu tasowa da kwararru na kawancen Sin da Afirka da aka bude a jiya Alhamis a birnin Johannesburg da ke kasar Afirka ta Kudu, zai lalubo hanyoyin karfafa hadin gwiwa, da fadada yin magana da murya daya a tsakanin kasashe masu tasowa da kuma habaka gudanar da tsarin shugabancin duniya na bai-daya.

Wanda kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da Tarayyar Afirka (AU) da kamfanin Independent Media na kasar Afirka ta Kudu da sauran abokan hulda suka shirya, taron na kwanaki biyu ya samu halartar wakilai sama da 200 daga kafofin watsa labarai fiye da 160, da kungiyoyin kwararru, da hukumomin gwamnati da sauran cibiyoyi daga kasar Sin da kasashen Afirka 41, da kuma kungiyar AU.

A karkashin taken “garambawul ga tsarin shugabancin duniya: sabbin rawar da za a taka da kudurori na hangen nesa ga hadin gwiwar Sin da Afirka,” taron ya mayar da hankali ne kan yadda hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai da kungiyoyin kwararru zai iya ba da gudummawa wajen tsara shugabanci na duniya mafi adalci da ya hade kowa da kowa.

ADVERTISEMENT

Taron ya kuma kunshi fitar da wani rahoto na kwararru mai taken “gina sabon tsarin shugabancin duniya–yin aiki tare don neman samar da tsarin shugabancin duniya mai adalci da ma’ana,” da kuma kaddamar da turbar sadarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa mai lakabin “hadin kai a cikin zukata, hanya da kuma aiki–shirin aiki kan karfafa hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2026.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta November 14, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G November 14, 2025 Daga Birnin Sin Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne November 14, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tsarin shugabancin duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan

Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Dr. Masoud Pezeshkian, ya isa babban birnin Kazakhstan, Astana, bisa gayyatar takwaransa na Kazakhstan.

Mataimakin Firayim Minista na Kazakhstan ya tarbi Shugaba Pezeshkian a filin jirgin saman Astana. Wannan ziyarar ta zo ne  bisa gayyatar shugaban Kazakhstan, wadda ke da nufin yin tattaunawa ta musamman tsakanin kasashen biyu.

A daya bangaren kuma Jakadan Iran a Moscow, Kazem Jalali, ya sanar da shirin ganawa tsakanin Shugaban Iran Masoud Pezeshkian da Shugaban Rasha Vladimir Putin a Turkmenistan.

Wannan ya zo ne a lokacin ziyarar da Putin ya shirya kaiwa zuwa Ashgabat a ranakun 11 da 12 ga Disamba don halartar wani taron tunawa da Ranar Zaman Lafiya da Aminci ta Duniya.

Kasashen Iran da Rasha dai sun kara bunkasa harkokinsu an tsaro da ayyukan soji a cikin watannin baya-baya nan, duk da cewa akwai tsohuwar alaka ta soji a tsakanin kasashen biyu, amma dai a halin yanzu alakar tana samun ci gaba a cikin sauri da ba a taba ganin irinsa ba, wanda kuma ake ganin hakan ba zai rasa nasaba da irin halin Rashin tabbas da ake ciki yankin ba, inda kasashen biyu kawayen juna suke yin aiki kafada da kafada domin tukarar duk wani kalubale.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5  December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu
  • Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan