Aminiya:
2025-11-13@17:01:21 GMT

An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya

Published: 13th, November 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da safarar bilAdama wadanda aka ceto yara 17 daga hannunsu a garin Zariya.

Wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ta bayyana cewa yaran da aka ceto ana zargin an shirya safarar su ne zuwa Abuja da wasu sassan ƙasar da ma ƙetare.

An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe Atiku ya karyata ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUV

Sanarwar ta bayyana cewa “an tari hanzarin ababen zargin ne da misalin ƙarfe huɗu na yammacin ranar 12 ga watan Nuwamba.

“A wannan lokaci ne jami’an sashen Ɗan Magaji da ke Zariya suka kai samame bayan samun rahoton cewa wasu mutane na shirin safarar yara da ke tafe a ƙarƙashin gadar Ɗan Magaji da ke unguwar Wusasa.

Ya bayyana cewa “waɗanda ake zargin sun haɗa da Musa Shu’aibu, mai shekara 21 daga Funtua, Jihar Katsina; Sani Mamman, mai shekara 23 daga Ingawa, Jihar Katsina; da Mubarak Ismail, mai shekara 20 daga Unguwa Uku ta Jihar Kano.

Kakakin ya ce, yayin bincike waɗanda ake zargin sun amsa cewa su ne suka tattaro yaran daga wurare daban-daban da zummar kai su Abuja kafin jami’an ’yan sanda su damƙe su.

DSP Hassan ya ƙara da cewa, yaran duk ƙanana ne, kuma suna cikin ƙoshin lafiya da yanzu haka suna hannun rundunar, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano iyayensu ko masu kula da su.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da bajintar jami’an sashen Dan Magaji, inda ya nanata cewa rundunar ba za ta lamunci duk wani nau’in safarar yara ko cin zarafin su ba.

Ya kuma shawarci iyaye da masu kula da yara da su ci gaba da lura da lafiyar da walwalar ’ya’yansu, tare da faɗakar da su kan haɗarin safarar yara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kaduna Safarar Yara Zariya safarar yara

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi

Gwamnatin Jihar Kwara ta jaddada kudirinta na ba da ingantaccen kulawa da kuma ƙarfafa matakan rigakafi ga waɗanda suka tsira daga cin zarafin jima’i da na jinsi (SGBV) a fadin jihar.

Kwamishiniyar Harkokin Mata, Hajiya Opeyemi Afolashade, ce ta bayyana haka yayin ziyarar sa ido da tantance ayyuka a Cibiyoyin Tallafawa Wadanda Aka Yi wa Cin Zarafi (SARCs) da ke Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Kwara (KWASU) a Ilorin da kuma Asibitin Kwarari ta Sobi da ke Alagbado.

Kwamishiniyar ta bayyana cewa cibiyar an kafa ne tare da hadin gwiwar ofishin Uwargidar Gwamna, domin jinya kyauta da kuma kwantar da hankali, da tallafi ga wadanda suka tsira daga cin zarafi a jihar.

Afolashade ta ƙara da cewa bincike da tantancewar da ake yi yanzu zai taimaka wajen tantance ingancin kulawar da ake bayarwa, da gano wuraren da ake bukatar gyara domin samar da tsarin taimako mai inganci da niyya kai tsaye ga masu bukata.

Ta kuma jaddada bukatar ƙara haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki tare da horar da ma’aikatan cibiyoyin SARC a fannin tattara bayanai da bayar da rahoto domin inganta tsarin tallafi ga wadanda suka tsira daga cin zarafin jinsi.

Ali Muhammad Rabiu/Ilorin

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Dillalin Makamai A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe
  • Sarkin Musulmi ya ba wa makarantu tallafin N1.3bn a Kebbi
  • Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata
  • EFCC na neman tsohon Gwamnan Bayelsa ruwa a jallo