Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
Published: 25th, November 2025 GMT
’Yan Majalisar Tarayya daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.
Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.
Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.
Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.
A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.
Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.
Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.
Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bukatar Gafarar Yan Majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno
Mayaƙan ISWAP sun sace wasu ’yan mata a Ƙaramar Hukumar Askira-Uba a Jihar Borno.
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdullahi Askira, ya tabbatar da sace ’yan matan.
Ɗalibai 50 da aka sace a Neja sun kuɓuta — CAN An rufe duk makarantu a KebbiYa ce an sace ’yan natan ne yayin da suke aiki a gonakinsu da ke yankin Mussa.
A cewarsa, ’yan matan guda 13 masu shekaru tsakanin 15 zuwa 20 sun tafi gona domin girbe amfanin gonarsu, sai maharan suka yi awon gaba da su.
Tun da farko an mayar da mutanen Huyim zuwa Mussa saboda matsalar rashin tsaro a garuruwansu.
Sai dai ya ce ɗaya daga cikin ’yan matan da aka sace ta tsere kuma ta koma gida a safiyar ranar Lahadi, amma sauran 12 har yanzu suna hannun maharan.
Sanata Mohammed Ali Ndume, wanda ke wakiltar yankin, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su ceto ’yan matan cikin ƙoshin lafiya.
Ya kuma roƙi al’ummar yankin da su ci gaba da yin addu’a, tare da sanar da hukumomi duk wani abun zargi.