Aminiya:
2025-11-28@20:12:46 GMT

Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko

Published: 28th, November 2025 GMT

Kasar Portugal ta kafa tarihi a birnin Doha na Qatar bayan da ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 (U-17) a karon farko, inda ta doke Austria da ci 1-0 a wasan ƙarshe.

An jefa ƙwallon da ta bai wa Portugal nasara ne ta hannun Anisio Cabral, wanda ya ci a minti na 32 da fara buga wasan a filin wasa na Khalifa.

Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi

A hanyarta ta kaiwa  wasan ƙarshen, Portugal ta doke Brazil a wasan kusa da na ƙarshe, yayin da Austria ta fitar da Italiya bayan lallasa ta da ci 2-0.

Wannan nasara ita ce ta farko a tarihin Portugal tun da aka fara gasar, wanda hakan ya sanya sunanta cikin jerin ƙasashen da suka taɓa ɗaga kofin.

Nijeriya ce ƙasa mafi nasara a gasar U-17, inda ta lashe ta sau biyar. Sai Brazil wacce ta lashe sau uku, Ghana da Mexico wadanda suka lashe sau biyu-biyu.

Akwa kuma Jamus, Ingila, Switzerland, Faransa da Saudiyya kuwa kowacce ta lashe sau daya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kofin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta samu nasara a wasan mako na 14 na Nigeria Premier Football League (NPFL), bayan da ta doke Ikorodu City da ci 2–1 a filin wasa na Muhammad Dikko, da ke birnin Katsina.

Wannan ita ce nasara ta uku da Pillars ta samu a kakar bana, cikin wasanninta 14, inda ta yi kunnen doki uku, sannan ta sha kashi shida.

’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Kafin wannan wasan, Kano Pillars ta yi wasanni takwas a jere ba tare da samun nasara ba.

Pillars ta zura kwallayenta ne ta hannun Rabiu Ali, wanda ya zura ta farko a minti na 3, sai Olakunle Alaka ya kara ta biyu a minti na 30.
A daidai minti na 45, kafin a je hutun rabin lokaci, Joseph Arumala ya rage tazara ga Ikorodu City.

Duk da wannan nasarar, Kano Pillars ta ci gaba da zama a matsayi na 20, inda take da maki 9 a ƙasan teburin gasar.

A wani labarin, ƙungiyar Katsina United ta samu nasarar doke Enyimba da ci 3–2 a birnin Ilorin, inda take buga wasanninta na gida bayan dakatar da ita daga yin wasa a filin gidan ta a Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • CAF Tayi Watsi Da Alƙalan Wasan Nijeriya a Kofin Afrika Na 2025
  • Ƙasar Japan ta fara sayar da injin da ke yi wa mutane wanka
  • Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba