Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-22@16:56:50 GMT

Gwamnatin Neja Ta Rufe Makarantu Saboda Matsalar Tsaro

Published: 22nd, November 2025 GMT

Gwamnatin Neja Ta Rufe Makarantu Saboda Matsalar Tsaro

Daga Aliyu Lawal 

Gwamnatin Jihar Neja ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da na masu zaman kansu a fadin jihar sakamakon sace dalibai da aka yi a Makarantar St. Mary’s Catholic School da ke Papiri a Karamar Hukumar Agwara.

Gwamna Mohammed Umar Bago ne ya sanar da hakan a Minna bayan wata tattaunawar tsaro gaggawar  ta da aka gudanar da shugabannin hukumomin tsaro, malaman addini da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya ce matakin ya zama wajibi domin kare rayukan dalibai yayin da ake kara kokarin ceto yaran da aka sace.

Gwamna Bago ya jaddada cewa yanzu lokaci ne na daukar mataki a maimakon zargin juna, inda ya bayar da umarnin cewa a rufe dukkan makarantun mishan, da na Islamiyya da kuma kwalejojin gwamnati na tarayya har sai wani lokaci.

Haka kuma ya umurci a rufe dukkan manyan makarantu da ke yankin Neja ta Arewa da wasu yankuna masu hadari a Neja ta Gabas.

Gwamnan ya bukaci hukumomin tsaro, kungiyoyin fararen huhula, na kwadago da shugabannin addini su mayar da hankali wajen aikin ceto, yana mai tabbatar da kudirin gwamnati na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Yayin da yake bayyana lamarin a matsayin “abin bakin ciki da takaici,” Gwamna Bago ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da yin addu’a.

Ya ce har yanzu ba a tabbatar da yawan daliban Makarantar St. Mary’s Catholic School da aka sace ba, domin jami’an DSS, Rundunar ‘Yan Sanda da sauran hukumomin tsaro na kan aiki don tantance sahihin adadin daliban da abin ya shafa.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rufe Makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana 47 da ke faɗin Najeriya.

Gwamnatin ta ɗauki wannan mataki ne bayan hare-haren da ’yan bindiga suka kai makarantu a jihohin Kebbi da Neja, inda suka sace ɗalibai da ma’aikata, suka kashe mutum ɗaya.

Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja

A wata takarda da aka aike wa shugabannin makarantu a ranar Juma’a, Daraktar Makarantun Sakandare, Hajiya Binta Abdulkadir, ta ce Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya amince da rufe makarantun na wucin gadi saboda barazanar matsalolin tsaro.

Takardar ta bayyana cewa an rufe makarantun ne domin kare ɗalibai da malamai daga hare-haren ’yan bindiga, da kuma kauce wa duk wata barazana.

Makarantun da abin ya shafa sun haɗa da waɗanda ke Zariya, Daura, Sakkwato, Potiskum, Ikare-Akoko, Abaji, da sauransu.

Wannan umarni na zuwa ne a daidai lokacin da hare-haren da ake kai wa makarantu ke ƙara tsananta.

A Jihar Kebbi, ’yan bindiga sun kai hari makarantar Government Girls Comprehensive Secondary School da ke Maga, inda suka sace ɗalibai 25, tare da kashe mataimakin shugaban makarantar, Malam Hassan Makaku, yayin da yake ƙoƙarin kare su.

Rahotanni sun nuna cewa daga 2014 zuwa 2022, an sace yara sama 1,680 a makarantun Najeriya.

Gwamnati ta ce rufe makarantun na wucin gadi ne, domin kare ɗalibai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Ba da Umarnin Rufe Makarantu 41 Nan Take
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta
  • Nigeria: An Rufe Makarantun Kwana A Jahar Kwara Saboda Matsalar Tsaro
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro