An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
Published: 23rd, November 2025 GMT
Hukumar Ilimi ta Matakin Farko ta Jihar Filato (PSUBEB) ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati a faɗin jihar sakamakon fargabar tsaro da ta taso a kwanakin nan.
A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce za a rufe ƙananan makarantun sakandare tun daga Asabar, 22 ga Nuwamba, 2025, yayin da makarantun firamare za a rufe su daga Litinin, 24 ga Nuwamba, 2025.
Wannan mataki na zuwa ne bayan sace ɗalibai a wasu makarantu da ke jihohin Kebbi da Neja a ‘yan kwanakin da suka gabata, abin da ya tayar da hankalin iyaye da hukumomi.
PSUBEB ta sanar da cewa rufe makarantun mataki ne na wucin-gadi domin daƙile duk wata barazana da ka iya tasowa, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar lafiya da tsaron ɗalibai da muhimmanci.
Hukumar ta buƙaci Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi, shugabannin makarantu da shugabannin al’umma da su ba da cikakken haɗin kai wajen aiwatar da umarnin, tare da zama masu kula da duk wata alama ta rashin tsaro a yankunansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Jihar Neja Makarantun Firamare Makarantun Sakandire matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
Gwamnatocin jihohin Katsina da Taraba sun ba da umarnin rufe makarantu sakamakon hare-haren ’yan bindiga da suka sace daruruwan ɗalibai a makarantu a cikin mako guda a jihohin Kebbi da Neja.
Gwamnatin Jihar Taraba ta rufe makarantun kwana a fadin jihar, inda ta ba da umarnin a koma tsarin jeka-ka-dawo sakamakon tabarbarewar tsaro.
Gwamnan Agbu Kefas, ya umarci duk makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu da dalibai su daina kwana a makarantu saboda fargabar tsaro a faɗin ƙasar.
Sanarwar da kwamishinar ilimi ta jihar, Augustina Godwin, ya fitar ta ce garkuwa da ɗalibai a Kebbi da Neja ta sanya daliban makarantun kwana zama cikin hadari.
Don haka gwamnati ta umarci komawa tsarin jeka-ka-dawo har sai tsaro ya inganta.
Hakan na zuwa ne a yayin da Gwamnatin Jihar Katsina ta bayar da sanarwar rufe dukkan makarantun gwamnatin, har sai abin da hali yayi.
Sanarwar da ta fito daga Hukumar Ilimin Firamare da Sakandaren jihar a ranar juma’a ta ce, ya ce makarantun za su kasance a rufe har sai an ga ci-gaban da aka samu na yanayin matsalar tsaron da ake fuskanta.
Gwamnatin tace tana nan tana bibiyar yadda sha’anin tsaron yake gudana kafin ɗaukar mataki na gaba.
Waɗannan matakai na zuwa ne bayan ’yan bindiga sun sace ɗalibai kimanin 340 a cikin mako guda a makarantun kwana a jihohin Kebbi da Neja.
A ranar Juma’a aka sace ɗalibai da malamai 315 a makarantar kwana ta St Mary da ke Jihar Neja, kwana huɗu bayan a ranar Litinin sun sace dalibai mata 26 suka kashe jami’an tsaro biyu a makarantar ’yan Mata ta Gwamanti GGCSS da ke yankin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu ta Jihar Kebbi.