Aminiya:
2025-11-24@06:49:13 GMT

NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki

Published: 24th, November 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A shekarar 2014, bayan tashin hankalin da ya biyo bayan sace ɗaliban Chibok da kuma yawaitar hare-hare kan makarantun yankin Arewa maso Gabas, gwamnatin tarayya tare da haɗin gwiwar ƙasashen duniya ta ƙaddamar da wani muhimmin shiri mai suna Safe School Initiative.

 

Manufar wannan shiri ita ce tabbatar da cewa dalibai suna iya zuwa makaranta cikin tsaro ba tare da fargabar hare-hare daga ‘yan ta’adda ko ‘yan bindiga ba.

NAJERIYA A YAU: Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne akan wannan shiri da kuma halin da yake ciki a wannan lokaci.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro

Hukumar Ilimi ta Matakin Farko ta Jihar Filato (PSUBEB) ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati a faɗin jihar sakamakon fargabar tsaro da ta taso a kwanakin nan.

A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce za a rufe ƙananan makarantun sakandare tun daga Asabar, 22 ga Nuwamba, 2025, yayin da makarantun firamare za a rufe su daga Litinin, 24 ga Nuwamba, 2025.

H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar

Wannan mataki na zuwa ne bayan sace ɗalibai a wasu makarantu da ke jihohin Kebbi da Neja a ‘yan kwanakin da suka gabata, abin da ya tayar da hankalin iyaye da hukumomi.

PSUBEB ta sanar da cewa rufe makarantun mataki ne na wucin-gadi domin daƙile duk wata barazana da ka iya tasowa, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar lafiya da tsaron ɗalibai da muhimmanci.

Hukumar ta buƙaci Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi, shugabannin makarantu da shugabannin al’umma da su ba da cikakken haɗin kai wajen aiwatar da umarnin, tare da zama masu kula da duk wata alama ta rashin tsaro a yankunansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
  • Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin