Aminiya:
2025-11-28@08:42:26 GMT

An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun

Published: 28th, November 2025 GMT

Babban Sufeton ’yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya ce sun janye ’yan sanda 11,566 da ke rakiyar manyan mutane kamar yadda Shugaban Ƙasa ya ba da umarni a kwanakin baya.

Ya kuma ce an sake tura waɗannan jami’an zuwa muhimman wuraren da aka fi buƙatars su don kare al’ummomi masu rauni a fadin ƙasa.

NAJERIYA A YAU:Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra

Aminiya ta rawaito cewa Shugaba Bola Tinubu, a ranar Lahadi, ya bayar da umarnin janye jami’an ‘yan sanda daga aikin tsaron manyan mutane tare da umartar a sake tura su zuwa ayyukan tsaro na asali.

Umarnin ya biyo bayan taron tsaro da aka gudanar a Abuja tare da shugabannin rundunonin tsaro da shugaban hukumar tsaro ta DSS.

Yayin da yake jawabi a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja, ranar Alhamis, lokacin da ya gana da manyan jami’an ‘yan sanda masu mukamin kwamishina, Egbetokun ya ce jami’an da aka janye za a mayar da su ga ayyukan tsaro na asali.

Ya ce shawarar janye jami’an daga aikin tsaron mutanen ba ta samo asali daga son rai ba, sai dai daga bukatar gaggawa ta karkatar da ma’aikata zuwa wuraren da tsaron jama’a ya fi bukata.

A cewarsa, wannan mataki ya yi daidai da babban aikin Hukumar ‘Yan Sanda ta Najeriya, wato kare ‘yan ƙasa, al’ummomi da kuma tabbatar da zaman lafiya, yana mai jaddada cewa dukkan jami’an 11,566 da aka janye an sake tura su wuraren aiki.

“A bisa umarnin Shugaban Ƙasa, mun janye jami’an 11,566 daga aikin tsaron manyan mutane. Waɗannan jami’an za a sake tura su zuwa muhimman ayyukan tsaro nan take,” in ji shi.

Babban Sufeton ya ce janyewar za ta bai wa ‘yan sanda damar ƙara yawan jami’an da za su yi aiki wajen tsaron ƙauyuka da birane, kare jama’a da yawa, ƙarfafa sintiri, ayyukan tsaro bisa bayanan sirri, da kuma daƙile barazanar tsaro cikin gaggawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Kayode Egbetokun manyan mutane ayyukan tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta zargi dan jarida kuma mai shiga tsakani da ’yan ta’addar da suka sace fasinjojin jrigin kasan Kaduna-Abuja a shekarar 2022, Tukur Mamu, da karbar Naira miliyan 50 daga kudin fansar fasinjojin.

Ana zargin Tukur Mamu da karbar kudin ne daga jagoran ’yan bindigar da ake kira da “Shugaba”.

Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000 Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi

Mamu na fuskantar tuhumar laifukan ta’addanci, ciki har da karɓar kuɗin fansa daga iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a harin jirgin Kaduna na ranar 28 ga Maris, 2022, hulɗa da kuɗaɗen ’yan ta’adda, hana aikin kwamitin babban hafsan tsaron kasa da aka kafa domin tattaunawa da masu garkuwa da mutanen, musayar saƙonnin murya da mai magana da yawun Boko Haram, da sauransu.

A ci gaba da shari’ar a ranar Talata, shaida na hukumae ta DSS na shida ya shaida wa kotu cewa ƙungiyar ta’addan ta nemi Mamu ya koya musu yadda ake buɗe shafin yanar gizo domin gudanar da ayyukansu.

Tun da farko, DSS ta bayyana cewa Mamu ya ba da shawara ga ƙungiyar ’yan ta’addan da su tattauna kai tsaye da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su, ba tare da shiga kwamitin babban hafsan tsaron da gwamnatin tarayya ta kafa ba.

Shaidar ya yi wannan bayani ne yayin fassara saƙonnin murya na Mamu a lokacin da ake yi masa tambayoyi a ƙasar Masar kafin a dawo da shi Najeriya.

A halin yanzu, Mamu ya shigar da Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN) kara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa kiran shi da dan ta’adda.

Ya ce ya shigar da ƙarar ce kan kiran nasa da dan ta’adda da ministan ya yi, alhali ana tsaka da shari’ar tuhumar laifukan ta’addanci kuma har yanzu ba a kai ga yanke hukunci ba.

Alƙali ya dage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Fabrairun 2026, domin amincewa da jawaban ƙarshe na ɓangarorin da abin ya shafa bisa tanadin Sashe na 49 na Dokar da kuma Sashe na 36 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia