Aminiya:
2025-11-28@21:45:15 GMT

Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata

Published: 29th, November 2025 GMT

Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Gombe ƙarƙashin Kwamishina, Asma’u Muhammad Iganus, ta ziyarci masarautun Nafada da Funakaye domin ƙaddamar da kwamitocin yaƙi da cin zarafi ga mata da yara.

A ziyarar ta farko a Masarautar Nafada, Kwamishiniyar ta ce alƙaluma sun nuna cewa cin zarafi ya kai kashi 87.

46 a jihar.

Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi

Ta ce ya ce ya zama dole a haɗa kai da sarakunan gargajiya don kawar da matsalar.

Sarkin Nafada, Alhaji Muhammad Dadum Hamza, ya yi tir da yawaitar laifukan aikata fyaɗe a yankin.

Ya bayyana cewa babu wani gurbi da mai laifin aikata fyaɗe zai samu mafaka.

Ya ce za su tabbatar da an hukunta duk wanda aka kama, tare da goyon bayan ƙarin hukuncin ɗaurin sama da shekaru 14 da doka ke yi a yanzu.

A Masarautar Funakaye, Sarkin Funakaye, Alhaji Yakubu Muhammad Kwairanga IV, ya nuna cikakken goyon bayansa ga matakin gwamnati.

Ya ce ba za a yi wa masu aikata fyaɗe sassauci ba, domin hukunci mai tsanani shi ne zai rage aikata laifin.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Funakaye, Alhaji Abdurrahman Shua’ibu Adam, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da aiki tare da ma’aikatar domin kare mata da yara.

Kwamishiniyar, ta miƙa kundin Dokar VAPP ga masarautar Funakaye domin fara aiki da shi kai-tsaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Kwamishiniya masarautu Sarakunan Gargajiya ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.

An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A

An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.

Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.

Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.

A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.

Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.

A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.

Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.

Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.

Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.

Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna