Aminiya:
2025-11-13@22:58:46 GMT

HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya

Published: 14th, November 2025 GMT

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen Jihar Kaduna, ta ƙone fiye da tan 52,000 na miyagun ƙwayoyi a bainar jama’a a ƙauyen Karofi da ke Kufena, a kan tsohuwar hanyar Birnin Gwari da ke Zariya.

An gudanar da bikin ƙone kayan ne a wannan Alhamis ɗin, inda Birgediya Janar Buba Marwa (Rtd.

), Shugaban NDLEA kuma Babban Jami’in Gudanarwa, ya jaddada cewa hukumar ta duƙufa domin kawar da barazanar miyagun ƙwayoyi daga cikin al’umma.

Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike Bebejin Katsina, Alhaji Nuhu Yashe ya rasu

Ya bayyana cewa, “Miyagun ƙwayoyi suna lalata tarbiyyar matasa a hankali, ba tare da an farga ba. Kowace tan ɗaya da aka ƙone, an ceto rayukan mutane da dama daga halaka.”

Shugaban hukumar, wanda Mataimakin Daraktan Harkokin Miyagun ƙwayoyi, Suleiman Ningi, ya wakilta, ya yi gargadi ga masu safarar miyagun ƙwayoyi da su daina kasuwancin kayan haram, su koma safarar kayan halal, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.

Janar Marwa ya ce NDLEA na ci gaba da fatattakar manyan dillalan miyagun ƙwayoyi da ƙungiyoyin su, tare da ƙarfafa wayar da kai a kan illolin kayan laifi.

Ya yaba wa rundunar NDLEA ta Jihar Kaduna bisa ƙoƙarinta, tare da gode wa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, saboda goyon bayan da yake bayarwa, ciki har da ba da motocin aiki da fili domin gina bariki ga hukumar.

Shugaban NDLEA ya roƙi iyaye, shugabannin al’umma da na addini, da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan mutane kan illar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, yana mai cewa, “Yaƙin da ake yi da miyagun ƙwayoyi yaƙin ceto rayuka da makomar ƙasa ne.”

Kwamandan NDLEA na Jihar Kaduna, Mohammed Tukur, ya bayyana cewa bikin ƙone miyagun ƙwayoyi na nuna jajircewar hukumar wajen kare al’umma daga illolin sha da safarar su.

Ya ce wannan mataki shi ne “ƙarshe a jerin matakan aiwatar da doka”, domin tabbatar da cewa waɗannan ƙwayoyi masu haɗari sun ɓace gaba ɗaya daga hannun mutane, don hana su cutar da matasa ko ƙarfafa ayyukan laifi.

Kwamandan ya bayyana cewa miyagun ƙwayoyin da aka ƙone sun haɗa da Tramadol, Wiwi (Cannabis), da Hodar Iblis da an kiyasta darajar su za ta kai Naira biliyan biyar.

Ya bayyana cewa wannan gagarumar nasara ta samu ne sakamakon ƙoƙarin jami’an NDLEA tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro irin su sojoji, hukumar kwastam, DSS, da ‘yan sanda.

Ya ce, “Wannan aiki shaida ce ta gaskiya, riƙon amana, da ƙwarewar NDLEA. A yau, muna sake tabbatar da sakonmu cewa Jihar Kaduna ba mafakar masu safarar ko masu amfani da miyagun ƙwayoyi ba ce.”

Tukur ya jaddada biyayyarsu wajen dawo da zaman lafiya da kare makomar matasan jihar.

A nasa jawabin, Gwamna Uba Sani ya yaba wa NDLEA bisa ƙoƙarinta wajen ganin cewa an tsarkake Jihar Kaduna daga miyagun ƙwayoyi.

Gwamnan ya ce yawan ƙwayoyin da aka ƙone na nuna tsananin ƙoƙarin da ake yi wajen tabbatar da doka a jihar, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa dukkan hukumomin tsaro wajen yaƙi da laifuka da duk wata barazanar tsaron al’umma a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna Miyagun ƙwayoyi Zariya miyagun ƙwayoyi ya bayyana cewa Ya bayyana cewa Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano

Wani babban ɗan Kasuwar Singa da ke Jihar Kano, Alhaji Salisu Abdullahi, ya ce ya yi asarar kaya da kuɗinsu ya haura Naira miliyan 120 a gobarar da ta auku da safiyar ranar Alhamis, wadda ƙone shaguna da yawa.

“An kira ni da misalin ƙarfe 6 na safe, na garzaya zuwa kasuwa, sai kawai na tarar komai ya ƙone.

“Na karɓi kaya bashi a makon da ya gabata domin ci gaba da sayarwa. Yanzu ban san ta yadda zan tunkari masu kayan ba,” in ji shi.

Gobarar, wadda ta fara da misalin ƙarfe 5 na Asuba, ta ƙone shaguna 44 da dukiya mai tarin yawa.

Hukumar Kashe Gobara Jihar Kano, ta ce gobarar ta samo asali ne daga matsalar wutar lantarki a wani gini, wadda daga bisani ta yaɗu zuwa sauran shaguna.

Wani ɗan kasuwa, Musa Abdulhadi, ya ce gobarar ta yaɗu cikin ƙanƙanin lokaci ta yadda ba a samu damar ceto komai ba.

“Gobarar ta yaɗu cikin sauri ƙwarai; ba mu iya fitar da kaya ko ɗaya ba. Na yi asarar kaya na kimanin Naira miliyan takwas.

“Wannan abu ne mai raɗaɗi musamman a wannan mawuyacin hali na tattalin arziƙi da ake ciki,” in ji shi.

Hukumar kashe Gobara ta jihar ta bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kai agaji ya samo asali ne daga manyan motoci da suka toshe hanyoyin shiga kasuwar.

Duk da haka, jami’an hukumar sun samu damar dakatar da gobarar kafin ta bazu zuwa wasu gine-gine.

Wasu ’yan kasuwa sun ɗora laifin tashin gobarar kan amfani da tsohuwar wayar wutar lantarki da rashin kulawa.

Sun ce sun ta yi ƙorafi a baya amma ba a ɗauki mataki ba.

Sun roƙi gwamnati ta tabbatar da ana yin bincike akai-akai a kasuwanni domin kare rayuka da duniyoyin al’umma.

’Yan kasuwar da abin ya shafa sun roƙi Gwamnatin Jihar Kano da masu hannu da shuni da su taimaka musu.

Abdullahi, ya ce: “Muna kira ga gwamnati ta taimaka mana mu sake gina shagunanmu. Da

“Da dama daga cikinmu bashi muka ɗauki kaya domin mu sayar. Idan ba a taimaka mana ba, ba mu san yadda za mu yi ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya
  • Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano
  • Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Kaddamar da Sabuwar Cibiyar Kiwon Lafiya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
  • HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano