Mataimakin ministan harkokin waje na kasar Sin Sun Weidong ya gana da jakadan Japan a Sin Kishi Nobuo bisa umurnin gwamnatin kasar a jiya Alhamis, inda ya yi tsokaci a hukumance kan kalaman da firaministar Japan Takaichi Sanae ta yi game da kasar Sin.

Sun ya ce, batun Taiwan na da matukar muhimmanci cikin muradun Sin, kuma ba za a iya tauye shi ba.

Taiwan yanki ne na Sin, kuma harkokin Taiwan batu ne na cikin gidan Sin. Tsara yadda za a warware matsalar Taiwan aiki ne na kasar Sin, kuma ba za a yi katsalandan a kai ba. Bana ta cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da Sin ta yi da mamayar dakarun Japan da kuma yakin duniya na biyu na kin tafarkin murdiyya, da kuma cika shekaru 80 da fitar yankin Taiwan daga mulkin mallakar Japan tare da dawo da shi karkashin Sin.

Ya kara da cewa, a shekaru 80 da suka gabata, jaruman jama’ar Sin sun yi yaki na tsawon shekaru 14 domin nuna turjiya ga maharan Japan. A yau, duk wanda ya yi yunkurin katsalandan a harkokin dunkulewar Sin, ko shakka babu Sin za ta mayar da martani mai tsanani!

ADVERTISEMENT

Sun ya kuma bukaci Japan da ta yi tunani mai zurfi game da laifuffukanta na tarihi, ta daidaita kura-kuranta, kuma ta janye kalamanta marasa kyau, kuma ta dakatar da tafiya a kan hanyar da ba ta dace ba. In ba haka ba, Japan za ta dauki alhakin duk wani sakamako da ya biyo baya, kuma tabbas kaikayi zai koma kan mashekiya! (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G November 14, 2025 Daga Birnin Sin Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne November 14, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan  November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin ta kara azamar kirkiro da fasahar sadarwa mai karfin 6G a cikin ’yan shekarun nan, inda ta samu ci gaba a bangaren binciken fasalin tsarin fasahar ta 6G da kuma zayyanar hanyar sadarwarta, kamar yadda ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta zamani ta kasar ta bayyana a jiya Alhamis.

A yayin gudanar da taron bunkasa fasahar 6G na shekarar 2025, mataimakin ministan masana’antu da fasahar sadarwa ta zamani na kasar Sin Zhang Yunming ya bayyana cewa, yanzu haka kasar tana da muhimman fasahohi na kirkiro da fasahar sadarwar 6G sama da 300.

Zhang ya kara da cewa, kasar ta hada kan kamfanoni sama da 100 na cikin gida da na waje a fannin tsarin masana’antu, kuma ta gayyaci kamfanonin duniya su zo su shiga cikin gwajin da ake yi na fasahar 6G.

ADVERTISEMENT

Zhang ya yi nuni da cewa, a wannan shekarar an fara gudanar da cikakken bincike kan tabbatar da ingancin fasahar 6G, inda ya kara da cewa yanzu haka aikin kirkiro da fasahar 6G yana kan wani muhimmin mataki wanda ke bukatar hikima da kuma cimma matsaya guda. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne November 14, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan  November 13, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
  • Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya
  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 
  • Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
  • Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa