Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo
Published: 12th, November 2025 GMT
Fitaccen ɗan wasan ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya tabbatar cewa Gasar Kofin Duniya ta shekarar 2026 ita ce ta ƙarshe da zai buga a rayuwarsa ta ƙwallon ƙafa.
Ronaldo mai shekaru 40, wanda ya ci ƙwallo fiye da 950 a matakin kulob da ƙasarsa, ya ce yana shirin yin ritaya nan da shekara ɗaya ko biyu masu zuwa.
“Eh, tabbas wannan shi ne Kofin Duniya na ƙarshe da zan halarta. Zan kai shekara 41, kuma ina ganin wannan ne lokacin da ya dace na ajiye takalmi,” in ji shi a wata tattanawa a Saudiyya.
Ronaldo, wanda yanzu ke bugawa kulob ɗin Al-Nassr ta Saudiyya, ya ce yana fatan cimma burin zura ƙwallo 1,000 kafin ya yi ritaya gaba ɗaya daga tamaula.
Tsohon ɗan wasan Manchester United, Real Madrid da Juventus, shi ne kan gaba a tarihin cin ƙwallo a matakin ƙasa, inda ya zura ƙwallo 143 a tawagar Portugal.
Ronaldo ya fara buga Kofin Duniya a shekarar 2006, lokacin da Portugal ta kai matakin kusa da na ƙarshe amma ta sha kashi a hannun Faransa.
A halin yanzu, zaƙaƙurin ɗan wasan bai taɓa lashe Kofin Duniya ba, sai dai ya taimaka wa ƙasarsa ta lashe Gasar Euro ta 2016 da kuma UEFA Nations League har sau biyu.
Yanzu haka, tawagar da Roberto Martínez ke jagoranta tana daf da samun gurbin shiga gasar ta 2026 da za a gudanar a Amurka, Kanada da Mexico, idan ta doke Jamhuriyar Ireland ranar Alhamis.
Ronaldo wanda ya zama ɗan wasan farko da ya ci ƙwallo mafi yawa a tarihin cancantar Kofin Duniya da ƙwallo 41 ya ce ritayarsa ba za ta zama abu mai sauƙi ba.
“Zai yi wuya sosai. Zan iya kuka ma, domin ni mutum ne mai buɗaɗɗiyar zuciya. Amma lokaci ya kusa,” in ji shi a wata hira da ya yi a shirin Piers Morgan Uncensored.
Ronaldo ya koma Saudiyya daga Manchester United a ƙarshen shekarar 2022, inda rahotanni suka nuna yana samun kusan euro miliyan 200 duk shekara.
A watan da ya gabata, mujallar Forbes ta bayyana shi a matsayin ɗan wasan da ya fi kowa samun kuɗi a duniya, yayin da jaridar Bloomberg ta tabbatar da cewa ya zama ɗan wasan ƙwallon ƙafa na farko da ya zama biloniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Kofin Duniya Kofin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Gasar Karatun Alqur’ani Mai Tsarki ta Sheikha Hind Bint Maktoum
An fara matakin karshe na Gasar Karatun Alqur’ani Mai Tsarki ta Duniya karo na 26 a Hadaddiyar Daular Larabawa.
A cikin yanayi mai cike da ruhi da daukaka, cike da ruhin gasar Alqur’ani, matakin karshe na Gasar Karatun Alqur’ani Mai Tsarki ta Duniya karo na 26 ta Sheikha Hind Bint Maktoum ta fara, a cewar Al Ittihad.
Gasar, wacce Kyautar Karatun Alqur’ani Mai Tsarki ta Duniya ta Dubai ta shirya, ta fara ne a rana ta farko a hedikwatar kyautar tare da halartar mahalarta maza 11 daga Hadaddiyar Daular Larabawa.
Gasar ta kwanaki biyar ta kunshi nau’ikan haddace-rubuce daban-daban, ciki har da 30, 20, 10, 5, 3 da Juz’ 30 na Alqur’ani.
Mahalarta sun fito ne daga Hadaddiyar Daular Larabawa, Masar, Iran, Mauritania da Bangladesh, wadanda dukkansu ke zaune a Hadaddiyar Daular Larabawa. Wannan yana nuna muhimmancin gasar a gida da kuma rawar da take takawa wajen karfafa gwiwar masu haddace Alqur’ani da kuma nuna hazaka masu ban mamaki a Hadaddiyar Daular Larabawa.
Mahalarta nau’o’in haddar mabambantan za su fafata ne a karkashin kulawar wani alkalai na musamman wanda ya kunshi zababbun alkalai karkashin jagorancin Sheikh Dr. Abdullah Muhammad Al-Ansari, tare da Sheikh Dr. Mana Al-Nahdi da Sheikh Ahmed Musa a matsayin mambobi.
Mahalarta wannan rana ta farko sun hada da Arian Ali Tajuddin (Iran), Nasr Abdul Majid Metwally Amer (Masar), Atul Amr Hammadi (Mauritania), Rashed Ali Omar Abdullah Salem (UAE), Ali Saleh Al-Hadrami (UAE), Abdulrahman Saber Abdulshafi Muhammad Abu Ezz (Egypt), Mansour Salem Al-Kau Muhammad (UAE) Al-Qasaidi Al-Shehi (UAE), Askar Muhammad Al-Kurbi (UAE), da Ali Jaber Al-Raisi (UAE).
Masu shirya gasar sun jaddada cewa wannan gasa tana ɗaya daga cikin muhimman shirye-shiryensu na shekara-shekara wajen hidimar Alƙur’ani Mai Tsarki da kuma ƙarfafa asalin addini na gaskiya, wanda aka gudanar bisa ga hangen nesa na shugabannin Hadaddiyar Daular Larabawa don tallafawa Alƙur’ani Mai Tsarki da kuma shirya tsararrun masu karatu, masu haddace Alƙur’ani da waɗanda suka nuna halayen Alƙur’ani.
Za a ci gaba da gasar farko a cikin kwanaki masu zuwa tare da halartar mahalarta daga ƙasashe daban-daban.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Zaben Iraki: Gwaji don ‘yancin siyasa da kawo karshen tsoma bakin Amurka November 10, 2025 Iran da Rasha sun amince su kafa kawancen sufurin jiragen ruwa November 10, 2025 Iran ta nuna damuwa kan zaman tankiya tsakanin Afghanistan da Pakistan November 10, 2025 Iraki: Kashi 82.42% na Masu Kada Kuri’a ne Suka Fito Zaben ‘Yan Majalisa November 10, 2025 Maduro ya kirayi taron CELAC da ya yi tir da ayyukan tsokana na Amurka a yankin Caribbean November 10, 2025 Lebanon: Mutane 28 ne suka yi shahada a hare-haren Isra’ila tun daga watan da ya gabata November 10, 2025 Gwamnan Darfur: Babu zaman lafiya da masu yi wa al’ummar Sudan kisan gilla November 10, 2025 Araghchi : Iran na yunkurin warware rikicin Pakistan da Afghanistan November 9, 2025 Kasashen (AES) za su hanzarta kafa rundunar hadin gwiwa ta tsaro November 9, 2025 Najeriya: An yi zanga-zangar tir da barazanar Trump November 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci