Aminiya:
2025-11-28@15:18:14 GMT

Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka

Published: 28th, November 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana cewa yana shirin daina karɓar mutane daga “ƙasashe masu tasowa” gaba ɗaya, ciki har da Afirka, Asiya da sauransu.

Ya bayyana haka ne yayin wani taro da ya gudana a fadar shugaban Amurka.

Ƙasar Japan ta fara sayar da i njin da ke yi wa mutane wanka

A cewarsa, tsohon tsarin shige da fice na Amurka yana rage ƙarfin tsaron ƙasa kuma yana matsa wa makarantun gwamnati, asibitoci, da sauran hidimomin jama’a.

Trump ya ce yawan baƙin haure a Amurka ya kai mutane miliyan 53, sannan ya yi zargin cewa mutane daga ƙasashen da ke fama da rikice-rikice, laifuka, da miyagun ƙungiyoyi suna ta zuwa ƙasar.

Ya ce shigowar baƙi ya kawo rabuwar kawuna da matsaloli a Amurka.

Haka kuma ya yi zargin cewa masu katin zama ’yan ƙasar da ke da tsarin ƙaramin albashi na rikice-rikice.

Ya batar da misali da Jihar Minnesota, yana inda ’yan gudun hijira daga Somaliya suka cika ta

Ya ce “ci gaban ƙasa ya lalace,” amma ya bayyana matakan da zai ɗauka.

Ya kuma ce zai soke shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba wanda gwamnatin Biden ta bari ke faruwa.

Trump, ya ce burinsa shi ne rage yawan waɗanda yake ganin ba su da tasiri mai kyau ko kuma suna kawo matsala a ƙasar.

Ya ce “mayar da mutane ƙasashensu” shi ne kawai mafita mai ɗorewa.

Wannan sanarwa na zuwa ne bayan harin da aka kai a Washington, D.C, inda aka yi wa sojoji biyu rauni.

Hukumomi a ƙasar sun ce mutumin da ake zargi da kai harin, ya shiga Amurka a 2021 bayan ya taimaka wa sojojin ƙasar a Afghanistan, kuma an ba shi mafaka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya

Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.

IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.

Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji

“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.

“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”

Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.

Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia