Cibiyar Masu Binciken Adadi ta Nijeriya (NIQS) ta yi kira ga gwamnatin tarayya da Majalisar Dokoki ta Kasa da su samar da mafita wajen kayyade kudin hayar gidaje, musamman a manyan birane, kamar Abuja. Shugaban Cibiyar, QS Kene Nzekwe ne ya yi kiran a ranar Laraba a Abuja a wani taron manema labarai don tunawa da taron NIQS karo na 31 da kuma babban taron cibiyar na kasa.

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle Nzekwe, wanda ya bayyana cewa, Cibiyarsa tana bai wa gwamnati shawarwari amma ya nanata cewa, alhakin gwamnati ne ta ɗauki mataki da kuma daidaita kuɗin hayar. “Za mu ci gaba da kira ga gwamnati, da masu tsara manufofi, har ma da ‘yan majalisa, da su yi dokokin da ya dace a fannin harkokin gidaje.” In ji shi Ya koka da cewa, ta yaya za a bayar da hayar gida mai dakuna biyu a Abuja akan naira miliyan biyar?. Dole ne a sami doka don rike hannun masu bayar da hayar gidaje. ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle November 13, 2025 Manyan Labarai Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su November 13, 2025 Manyan Labarai Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba

Shugabannin jam’iyyar APC a matakin unguwanni 35 da sakatarorinsu a faɗin Jihar Kuros Riba, sun nemi a tsige shugaban jam’iyyar na jihar, Mista Alphonsus Eba, bisa zargin badaƙala da kuɗaɗen jam’iyya da kuma nuna son kai wajen gudanar da harkokin jam’iyyar.

Wannan buƙatar ta fito ne a cikin wata sanarwa da shugabanni da sakatarorin jam’iyyar suka rattaba wa hannu bayan taron da suka gudanar a garin Kalaba, babban birnin jihar, a ranar Talata.

Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno

Shugabannin sun bayyana cewa idan ba a ɗauki mataki kan shugaban ba, akwai yiwuwar rikicin cikin gida ya durƙushe jam’iyyar a jihar.

Da yake jawabi bayan taron, shugaban ƙungiyar shugabannin, Cif Kelvin Njong, ya shaida wa Aminiya cewa sun gamsu cewa shugaban jam’iyyar na jihar yana amfani da dukiyar jam’iyya yadda yake so ba tare da tuntubar kowa ba.

“Muna zargin shugaban jam’iyyar da wadaƙa da kuɗaɗen jam’iyya. Ba ya bin tsarin jam’iyya kuma ba ya jin shawarar kowa. Wannan ne dalilin da ya sa muke son a sauke shi domin a samu shugabanci nagari,” in ji shi.

Sun kuma zargi shugaban jam’iyyar da nuna bambanci da son kai ga wasu ’ya’yan jam’iyyar, lamarin da suka ce ya saɓa wa wasu sassa na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC da aka sabunta a watan Maris na 2022.

Haka kuma, shugabannin sun yi zargin cewa Alphonsus Eba ya ƙi raba kuɗaɗen da aka samu daga sayar da fom ga ‘yan takara a zaɓen 2023 yadda ya kamata, musamman ga shugabannin jam’iyyar a ƙananan hukumomi da mazabu.

“Akwai shugabanni da sakatarori har mutum 5,778 a matakai daban-daban, amma an ce naira miliyan 9.2 kawai aka raba daga cikin miliyoyin da aka tara.

“Shugabannin jiha su kaɗai ne aka bai wa naira miliyan 40. Wannan rashin adalci ne kuma ya saba da tsarin jam’iyya,” in ji su.

Sun kuma buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan yadda shugaban ya riƙa kashe kuɗaɗen jam’iyya da sunan ayyuka, tare da buƙatar a tabbatar da raba kaso 70 cikin 100 na kuɗaɗen jam’iyya ga ƙananan hukumomi, mazabu, da gundumomi.

Ɗaya daga cikin shugabannin jam’iyyar a ƙaramar hukumar Bekwarra, Kwamared Odama Thomas Odama, ya ce: “Abin da muke cewa gaskiya ne, ba bita-da-ƙulli muke yi masa ba. Shugaban ya ci amana kuma hakan ya jawo ɓacin ran ’ya’yan jam’iyyar.”

Shi ma sakataren ƙungiyar shugabannin jam’iyyar APC a matakin ƙananan hukumomi, William Book, ya jaddada cewa duk zarge-zargen da aka ambata gaskiya ne.

“Ba zargin na shaci faɗi muke yi masa ba, akwai hujjoji da takardu da ke tabbatar da abin da muke faɗi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • Hukumar Tsara Birane ta Kano Ta Fara Horar da Ma’aikata Kan Dokokin Aiki
  • An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
  • Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa
  • Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika
  • Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump