Aminiya:
2025-11-23@16:37:09 GMT

Ɗalibai 50 da aka sace a Neja sun kuɓuta — CAN

Published: 23rd, November 2025 GMT

Ɗalibai 50 da aka sace a Makarantar St. Mary’s da ke garin Papiri, a Ƙaramar Hukumar Agwara ta Jihar Neja, sun tsere daga hannun ’yan bindiga.

’Yan bindigar da suka sace su, sun kai hari makarantar da safiyar ranar Juma’a.

Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji An rufe duk makarantu a Kebbi

Maharan sun harbe mai gadin makarantar sannan suka sace ɗalibai sama da 200 da ma’aikatan makaranta 13, ciki har da malamai.

A farko, Shugaban Ƙungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) a Jihar Neja, Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ne mamallakin makarantar, ya ce ɗalibai 215 tare da ma’aikata 12 aka sace.

Sai dai a ranar Asabar, ya ce har yanzu ba inda ɗalibai 88 suke ba.

Amma a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Daniel Atori, ya fitar a madadinsa ranar Lahadi, Fasto Yohanna ya ce ɗalibai 50 sun tsere a ranar Asabar kuma sun koma gidajensu.

Sanarwar ta ce: “A ranar Lahadi, 23 ga watan Nuwamba 2025, mun samu labari mai daɗi cewa yara 50 sun tsere kuma sun koma wajen iyayensu.”

Rabaran Yohanna, ya bayyana cewa makarantar na da ɗaliban kwana da na jeka ka dawo, sashen firamare na da dalibai 430; inda sashen kwana ke da ɗalibai 377, na jeka ka dawo na da 53.

“A halin yanzu, ban da yara 50 da suka tsere, muna da yara 141 waɗanda ba a sace ba. Yanzu haka, yara 236 da ƙananan yara uku na ma’aikata, ɗalibai 14 na sakandare, da ma’aikata 12 na hannun maharan.”

Rahotanni sun nuna cewar hukumomin tsaro na ƙoƙarin ceto sauran da ke hannun ’yan bindiga.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai hari tserewa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta

Gwamnatin Jihar Neja ta tabbatar da sace ɗalibai da ma’aikatan makarantar Katolika ta Saint Mary da ke Papiri, da ke Ƙaramar Hukumar Agwara da jihar.

Aminiya ta rawaito yadda ’yan bindiga suka kutsa cikin makarantar tsakanin ƙarfe 2:00 zuwa 3:00 na safiyar Juma’a.

’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su

Shugaban Sashen bayar da Agaji na Ƙaramar Hukumar, Ahmed Abdullahi Rofia, ya tabbatar da harin ta wayar salula, amma bai bayar da cikakkun bayani ba.

Sai dai a cikin wata sanarwa, Sakataren Gwamnatin Jihar Neja, Abubakar Usman, ya ce bayan samun bayanan sirri tun da farko, gwamnati ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun kwana a yankin.

Sai dai ya  ce makarantar da abin ya shafa ta ƙi bin umarnin ta kuma buɗe makarantar.

“Gwamnatin Jihar Neja ta yi matuƙar bakin ciki da labarin sace ɗaliban makarantar St. Mary da ke Ƙaramar Hukumar Agwara. Har yanzu ba a tabbatar da adadin ɗaliban da aka sace ba yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da tantance lamarin.

“Jihar ta samu bayanan sirri tun da farko da ya nuna ƙaruwa barazanar tsaro a wasu sassan yankin arewa.”

“A kan haka ne Gwamnatin jiha ta bayar da umarnin dakatar da dukkan ayyukan gine-gine tare da rufe dukkan makarantun kwana a yankin da abin ya shafa a matsayin kandagarki

“Sai dai makarantar St. Mary ta ci gaba da zama a buɗe da ci gaba da karatu ba tare da sanarwa ko neman izini daga gwamnati ba.”

“Jami’an tsaro sun riga sun fara cikakken bincike da aikin ceto domin tabbatar da an dawo da ɗaliban gida lafiya.”

“Gwamnatin Jihar Neja tana aiki kai tsaye da dukkan hukumomin tsaro da abin ya shafa kuma za ta ci gaba da bayar da rahotanni yayin da bayani kara fitowa.”

“Gwamnati na kira ga masu makarantu, shugabannin al’umma, da duk masu ruwa da tsaki da su bi ƙa’idojin tsaro da aka bayar domin kare rayukan jama’a. Kariya ga rayuka, musamman na ’ya’yanmu, ita ce babban abin da wannan gwamnatin ta sa a gaba,” in ji shi.

A Jihar Kwara makwabciyar Nejan, gwamnatin jihar ta sanar da rufe makarantu fiye da 50 a kananan hukumomi hudu sakamakon sake ƙaruwar hare-hare a yankunansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta
  • ’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi