Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-13@10:09:46 GMT

Gwamna Nasarawa Ya Ce Za Su Samar da Masana’antu Don Ayyukan Yi

Published: 13th, November 2025 GMT

Gwamna Nasarawa Ya Ce Za Su Samar da Masana’antu Don Ayyukan Yi

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya bayyana cewa hangen nesansa na ƙarfafa masana’antu a jihar shi ne domin ƙirƙirar ayyukan yi da kuma inganta rayuwar jama’ar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Fadar Gwamnati ta Lafia, yayin da yake karɓar bakuncin sabbin shugabannin Ƙungiyar ‘Yan Jarida Masu aiko rahotann dake Jihar (Correspondents’ Chapel).

Ya ce baya ga jawo ‘yan kasuwa masu saka jari a fannin masana’antu da ma’adinai, gwamnatin sa tana kuma zuba jari mai yawa a harkar noma.

“Ɗaya daga cikin abubuwan da ke ba ni farin ciki shi ne harkar noman shinkafa. Ka san muna da wata ƙaramar gona mai girman hektare 3,300 domin noman shinkafa.

Ina alfahari da gonar shinkafar mu domin mun fara girbi, kuma dukkan alamu sun nuna cewa amfanin gona a wannan kakar ya fi na bara, musamman a yawan amfanin da ake samu a kowace hekta,” in ji shi.

Gwamna Sule ya ce yana da cikakkiyar niyya ta ƙaddamar da aikace-aikace da shirye-shirye da za su tabbatar da amfanin kai tsaye ga jama’ar jihar.

A cewarsa, ɗaya daga cikin dalilan da ke haifar da kalubale da rashin tsaro a arewacin ƙasar, shi ne mutane da yawa ba su da abin yi.

“Ka san wannan shi ne ɗaya daga cikin abubuwan da ke jawo matsalar tsaro.

A da, lokacin da muke yara, akwai masana’antar yadi (textile) a Kaduna da ƙananan masana’antu a sassa daban-daban na arewa, mutane suna da abin yi.

Ba a cika jin labarin rashin tsaro ba, domin mutane suna zuwa gona, suna yin aikinsu da halaltattun hanyoyi,” in ji gwamnan.

Yayin da yake taya sabbin shugabannin ƙungiyar ‘yan jarida murna bisa nasarar rantsar da su, Gwamna Sule ya kuma bukace su su tsaya kan ƙa’idar aikin jarida ta gaskiya da adalci.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida na Jihar Nasarawa, Alhaji Abubakar Abdullahi, ya ce ziyarar ta kasance ne domin gabatar da sabbin shugabanni ga gwamna da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da ‘yan jarida.

Ya yaba wa Gwamna Sule bisa aikace-aikacen ci gaba da gwamnatin sa ke aiwatarwa, musamman gona mai girman hekta 3,300 a Jangwa, karamar hukumar Awe, wadda amfanin shinkafar ta za ta shiga kasuwa a ƙarƙashin sunan alamar jihar “NASACCO Rice.”

Ya kuma ambaci wasu muhimman ayyuka da suka haɗa da gine-ginen gadar sama da ƙasa a Lafia, ayyukan gadar Keffi/Akwanga, sabuwar cibiyar ma’aikata ta jihar, da kuma biyan fansho da hakkokin ma’aikata a kan lokaci.

“Gwamnatinka tana ci gaba da nuna goyon baya ga ci gaban aikin jarida, kuma muna godiya da kyakkyawar dangantaka da muke da ita, tare da fatan za ta ci gaba da dorewa,” in ji shi.

Aliyu Muraki, Lafia.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Xiyara

এছাড়াও পড়ুন:

APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanya da kudinta ya kai Naira Biliyan 14 a Karamar Hukumar Malam Madori, wanda ke nuna jajircewar gwamnatinsa wajen bunkasa ababen more rayuwa1 karkashin shirin sabunta kudurori na gwamnatin tarayya wato “Renewed Hope Agenda.”

A yayin taron kaddamarwar, an kuma gabatar da sabbin motoci ga shugabannin jam’iyyar APC guda takwas da masu tallata jam’iyyar a mazabar Arewa maso gabashin jihar, wanda Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya dauki nauyi.

Wannan mataki na da nufin karfafa hadin kai a jam’iyyar da kuma tallata hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadin jihar.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya yaba da jajircewar Sanata Ahmed Malam Madori na nuna biyayya, karamci, da sadaukarwa wajen ci gaban jam’iyyar APC. “Wannan babbar shaida ce ta jajircewar Sanata Malam Madori ga jam’iyyarmu”.

 

Haka kuma Gwamnan ya karfafa gwiwar sauran mambobi da su tallafa wa shirin ci gaba na Shugaba Tinubu karkashin ‘Renewed Hope Agenda.”

Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya bayyana cewa tallafin motocin na nufin bai wa mambobin jam’iyya damar yin ingantaccen aiki wajen tallata shirin ci gaba na Shugaban kasa da kuma Shirin Ci Gaba na Gwamna Namadi.

“Shugaba Tinubu da Gwamna Namadi sun kawo gagarumin ci gaba ga al’umma da ababen more rayuwa a Jigawa. An amince da kafa muhimman hukumomin tarayya, ciki har da Cibiyar Horar da ‘Yan Sanda a Kafin Hausa, Kwalejin Ilimi ta Tarayya a Malam Madori, da Kwalejin Noma ta Tarayya a Kirikasamma,” in ji shi.

Ya jaddada ayyukan Gwamna Namadi na baya-bayan nan, ciki har da aikin hanyar kilomita 47 da ke hada Hadejia–Garun Gabas, inganta asibitoci, da farfado da cibiyoyin lafiya na farko.

Sanata Malam Madori ya kara da jaddada hadin kan masu ruwa da tsaki na APC a mazabar Arewa maso gabashin Jigawa, wanda ya hada da ‘yan majalisar wakilai guda uku, ‘yan majalisar jihar guda tara, shugabannin kananan hukumomi takwas, da ‘yan majalisar kananan hukumomi 85

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Ka’idoji Ga Samar da Injinan Noma a Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Shirya Faɗaɗa Gonakin Shinkafar Jangwa Don Ƙara Samar da Shinkafa
  • Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba
  • Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
  •  Babu Wani Zabi Da Ya Rage Face Amincewa Da Iran A Matsayin Cibiyar Kimiyyar Masana’antar Nukiliya
  • APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori