Aminiya:
2025-12-13@14:00:30 GMT

MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC

Published: 13th, November 2025 GMT

Kungiyar Kare Muradun Musulmai (MURIC) ta bukaci a gaggauta tsige Farfesa Joash Amupitan daga shugabancin Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), saboda matsayinsa kan batun rashin tsaro a Najeriya.

Aminiya ta rawaito cewa, a cikin wani rubutu a baya, Amupitan wanda a lokacin malami ne a Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya ce “abu ne sananne cewa ana aikata laifuka a ƙarƙashin dokokin kasa da kasa a Najeriya, musamman laifukan da suka shafi cin zarafin bil’adama, laifukan yaki da kuma kisan kare dangi.

Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano

Ya kara da cewa: “Kalma guda da hukumomin Najeriya da masu bincike na kasa da kasa da masu bayar da rahoto ba su ambata ba (ko kuma suka ki ambata) dangane da dogon rikicin da ake fama da shi a Najeriya ita ce ‘kisan kare dangi.’ Shin wannan mantuwa ce ta gangan ko kuskure ne?

“Zargin shiga tsakanin gwamnati da kungiyoyin da ba na gwamnati ba wajen aikata laifukan kasa da kasa a Najeriya ya kara dagula lamarin da tuni ya yi tsauri.

“Kungiyar Boko Haram tana da burin sauya Najeriya zuwa tsarin Musulunci. ’Yan bindigar kabilar Fulani, a nasu bangaren, sun shiga irin wannan rikicin na adawa da Kiristoci kamar yadda Boko Haram ke yi,” kamar yadda ya rubuta a lokacin.

Haka kuma ya kira Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, hukumomin majalisar da manyan kasashen duniya da su shawarci kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kisan kare dangi su kai Najeriya kotun kasa da kasa (ICJ) saboda gazawar ta wajen hana da hukunta kisan kare dangi kamar yadda aka tanada a cikin saɗarori na 8 da 9 na yarjejeniyar; sannan su yi la’akari da shigar dakarun Majalisar Dinkin Duniya, Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ko na ECOWAS a matsayin mataki na karshe, bisa ga saɗara ta 42 a Kundin Majalisar Dinkin Duniya.

To sai dai a cikin wata sanarwa da shugabanta, Farfesa Ishaq Akintola ya fitar, MURIC ta gargadi cewa duk wanda ya shafi irin wannan rubutu mai cike da cece-kuce ba za a iya amincewa da shi wajen jagorantar harkokin zabe ba a Najeriya.

“Mutumin da ya rubuta wasikar kiyayya ga Shugaba Donald Trump kan Musulmai a Arewacin Najeriya ba za a iya tsammanin adalci daga gare shi wajen gudanar da zabe a Najeriya ba,” in ji shi.

MURIC ta ce rawar da ake zargin shugaban INEC ya taka a cikin rahoton ta lalata amincewar da jama’a suka yi masa a baya kuma tana haifar da “barazana ga Musulmai ’yan takara a Arewa ta Tsakiya da sauran sassan kasar.”

“Tun daga lokacin da wannan bayani ya fito, Amupitan ya zama wanda Musulmai ba sa son ganin ya taka rawa a harkokin zabe. Muna bayyana cikakkiyar rashin amincewa da shi a matsayin shugaban INEC,” in ji kungiyar.

Kungiyar ta kuma bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya tsige shugaban INEC daga muƙaminsa tare da nada wanda zai samu karɓuwa a fadin kasa.

“Muna ba da shawarar cewa a zabi wani wanda ya cancanta, da zai samu karbuwa a fadin kasa, wanda zai fi dacewa ya kasance mai addini daya da Amupitan amma daga wani yanki daban na siyasa,” in ji Akintola.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zargin kisan Kiristoci kisan kare dangi

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa

Daga Usman Muhammad Zaria

Ma’aikatar mata da walwalar jama’a ta jihar Jigawa za ta kashe naira milyan dubu 10 da milyan 599 wajen gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a sabuwar shekara.

Kwamishinar ma’aikatar, Hajiya Hadiza Abdulwahab, ta bayyana hakan lokacin kare kiyasin kasafin kudin ma’aikatar a gaban kwamatin harkokin mata na majalisar dokokin jihar Jigawa.

A cewar ta, za su mayar da hankali wajen inganta shirye shiryen bunkasa rayuwar mata da al’amuran da su ka jibinci kananan yara domin bada kariya ga masu rauni a cikin al’umma.

Hajiya Hadiza Abdulwahab ta ce ma’aikatar ta samu nasarori wajen aiwatar da tanade tanaden kasafin kudin 2025, yayin da za su ci gaba da daukar matakan da su ka dace domin inganta ayyukan su a sabuwar shekara.

Ta kuma yi nuni da cewar, batun kula da rayuwar masu rauni a cikin al’umma ya kasance ginshiki daga cikin kudurorin Gwamna Malam Umar Namadi.

Hajiya Hadiza, ta bada tabbacin aiki tukuri domin samun nasarar da ake bukata a sabuwar shekara.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD