Daga Bello Wakili

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi labarin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi cikin alhini da jimami.

Fitaccen malamin da ke Bauchi ya rasu ne a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2026, yana da shekaru 101.

Shugaban Ƙasan ya yi jimamin rasuwar jagoran Darikar Tijjaniyya, yana bayyana shi a matsayin ginshiƙin ɗabi’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa da wa’azi.

Shugaba Tinubu ya ce rashinsa babban rashi ne ba ga iyalansa da dimbin mabiyansa kaɗai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

Shugaban Ƙasa ya tuna da albarka da goyon bayan da ya samu daga marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a lokacin yakin zaɓen 2023.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba, mai cike da natsuwa da hikima. A matsayinaa na mai wa’azi kuma masani kan tafsirin Alƙur’ani Mai Girma, yana da’awar zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga mabiyan Shehun a ci da wajen ƙasa  bisa wannan babban rashi.

Haka kuma ya ja hankalinsu da su girmama sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, ƙarfafa dangantakarsu da Allah, da kuma kasancewa masu taushin zuciya ga jama’a.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai

Daga Bello Wakili

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a duk fadin kasar, sakamakon karuwar kalubalen tsaro da ake fuskanta.

Shugaban ya ce za a dauki sabbin jami’an tsaro nan ba da jimawa ba, wadanda suka hada da na sojiin, ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro — domin karfafa matakan tsaron kasa.

A karkashin sabon umarnin, an bai wa Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ikon daukar karin jami’aaidubu ashirin,  wanda hakan zai kawo yawan sabbin  jami’an da za a dauka bana zuwa dubu hamsin.

Shugaban kasar ya kuma amince a yi amfani da sansanonin horas da matasa masu yi wa kasa  NYSC a matsayin wuraren horaswa na wucin gadi, sakamakon gyare-gyaren da ake yi a makarantun horar da ‘yan sanda a fadin kasar.

Haka zalika Jami’an da aka cire daga ayyukan tsaron manyan mutane za su samu horo na gaggawa kafin a tura su zuwa yankunan da ke da hadari.

Shugaban ya kuma bai wa Hukumar tsaro ta DSS umarnin gaggauta tura dakaru masu horo na musamman zuwa dazuka domin yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga. A don haka, hukumar ta DSS za ta dauki karin ma’aikata don karfafa wannan aiki.

Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya su bada hadin kai ga matakan tsaron da ake dauka.

Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ceto daliban Jihar Kebbi 24 da aka yi garkuwa da su, da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Niger da sauran wadanda ke tsare.

Shugaban ya umurci Rundunar Soji ta kara zafafa ayyuka a dukkan yankunan da ake rikici, tare da jaddada muhimmancin ladabi, gaskiya da kin amincewa da cin hanci ko sakaci.

Ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe a hare-haren da suka faru a Kebbi, Borno, Zamfara, Niger, Yobe da Kwara, tare da karrama jaruman sojojin da suka rasa rayukansu, ciki har da Birgediya-Janar Musa Uba.

Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da goyon bayansa ga jami’an saro na jihohi, tare da kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da ke son kafa ‘yan sandan jiha damar yin hakan.

Ya shawarci gwamnatocin jihohi su sake duba tsarin kafa makarantun kwana a wuraren da ke da nisa ba tare da wadatattun matakan tsaro ba, sannan ya yi kira ga cibiyoyin addini su kara inganta tsaron wuraren ibada.

Dangane da rikice-rikicen manoma da makiyaya, Shugaban ya bukaci kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo na zamani (ranching) tare da yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya ta hannun sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwo.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai