Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa dawowar ’yan mata 24 da ’yan ta’adda suka sace a Maga, Jihar Kebbi.

’Yan ta’addan sun kai hari makarantar  ranar 17 ga wantan Nuwamban 2026, inda suka yi awon gaba da ’yan matan, jim kaɗan bayan wata rundunar soji ta bar harabar makarantar.

Lamarin Kebbi ya haifar da wasu sace-sace makamanta a Eruku da ke Jihar Kwara da kuma Papiri a Jihar Neja.

An sako dukkan mutune 38 da aka sace a Eruku ranar Lahadi, inda a wannan ranar ce shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Jihar Neja ya ce an samu yara 50 daga cikin ɗaliban makarantar Katolika da suka ɓace a gidajen iyayensu.

Shugaba Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarin da suka yi wajen ganin an kubutar da dukkan mutanen da ’yan ta’adda suka sace.

Ya umarci jami’an tsaro da su ƙara ɗaukar matakan gaggawa don ceto sauran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

“Ina farin cikin cewa an samu dukkan ’yan mata 24. Ya zama wajibi mu ƙara tura jami’an tsaro  yankunan da ke da rauni don hana sake faruwar irin wannan lamari. Gwamnatina za ta bayar da dukkan tallafin da ake buƙata don cimma haka,” in ji Shugaba Tinubu.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000

Shugaban kasan Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin janye jami’an ƴansanda dake gadi ko rakiyar manyan mutane domin mayar da su aikin tsaro.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar ya fitar Mr Bayo Onanuga, da yammacin wannan Lahadi, ya ce daga yanzu za’a rika tura jami’an ƴansanda ne gudanar da ayyukan ƙasa.

Tinubu ya bayar da umarnin ne yayin ganawar da ya yi da shugabannin tsaron ƙasar da suka haɗa da rundunar sojin sama, da na ƙasa da na ruwa da Darakta Janar na ma’aikatar tsaro ta DSS da kuma Sufeto Janar na ƴansanda Kayode Egbetokun.

Sanarwar ta ce, daga yanzu duk mutumin da ke son jami’an tsaro su yi gadinsa to ya nemi jami’an tsaron Nigeria Security and Civil Defence Corps.

Shugaban ƙasa ya ɗauki wannan mataki ne la’akari da cewa sassan Najeriya da dama, musamman a yankunan karkara ana fuskantar ƙarancin jami’ai ofisohin ƴansanda, lamarin da ke sanya wahalar sauye nauyin kare al’umma da aka ɗaura musu.

Tuni Shugaba Tinubu ya amince da ɗaukar ƙarin jami’an ƴan sanda 30,000, yayin da gwamnatin tarayya ta sanar da wani shirin haɗin gwiwa da jihohi don haɓaka cibiyoyin horar da  ƴan sanda a duk faɗin ƙasar.

Daga BELLO WAKILI 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Sace ɗalibai: Idan Tinubu ba zai iya ba ya sauka kawai — PDP
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Sace ɗalibai: Ba rufe makarantu ba ne mafita — PDP
  • Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000
  • Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi