Aminiya:
2025-11-13@20:53:50 GMT

Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya

Published: 13th, November 2025 GMT

Tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya Super Eagles ta doke tawagar ƙasar Gabon a wasan neman tikitin shiga Gasar Kofin Duniya ta 2026 da suka fafata a yammacin wannan Alhamis.

Wasan wanda aka soma da ƙarfe 5 na yamma a filin wasa na Prince Moulay Hassan da ke Rabat a Morocco, ya bai wa Super Eagles damar lallasa The Panthers har ci 4-1.

Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya

Wannan sakamakon ya bai wa Nijeriya nasarar kaiwa zagayen ƙarshe a wasan cike gurbin shiga gasar Kofin Duniya na 2026.

Akor Adams ne ya fara ci wa Super Eagles ƙwallo a minti na 78, amma daga baya Gabon ta farke ta hannun Mario Lemina daf a tashi daga fafatawar.

A haka dai aka tashi 1-1 bayan minti 90 da suka buga, lamarin da ya sa aka yi ƙarin minti 30 saboda dole sai an samu wanda zai yi nasara.

Bayan an dawo daga hutun ƙarin lokacin ne aka ci gaba da fafatawar har ta kai ga Super Eagles ta ƙara na biyu ta hannun Chidera Ejuke, sannan Victor Osimhen ya ƙara na uku na hudu.

A ɗaya wasan daf da ƙarshen kuma, Kamaru ce za ta fafata da Jamhuriyar Congo a ranar Alhamis, inda duk wanda ya yi nasara a ciki, zai fuskanci tawagar ta Nijeriya a ranar Lahadi mai zuwa.

Wasan na yau dai shi ne na farko tsakanin ƙasashen tun bayan shekarar 2005, lokacin da Nijeriya ta doke Gabon da ci 2-0.

An barje gumin ne ƙasa da awanni 24 bayan tawagar Super Eagles da Hukumar Kwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) sun warware matsalolin da suka shafi kuɗaɗe tsakanin ‘yan wasa da hukumomin ƙwallon ƙafa.

Kyaftin William Troost-Ekong ya tabbatar da cewa an biya dukkan haƙƙoƙin da suke bi, inda ya ce tawagar ta koma fili cikin karsashi da ƙwarin gwiwar neman nasara a wasan yau.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana

Aƙalla mutum 12 sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata a wani turmutsutsu da ya faru yayin jarabawar ɗaukar aikin soja a Filin Wasa na El-Wak da ke Accra, babban birnin ƙasar Ghana.

Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, yayin da ɗaruruwan matasa masu neman aikin suka kutsa cikin filin wasan ba tare da bin tsarin shiga da aka tanada ba.

An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo

Rundunar Tsaron Ghana (GAF) ta ce mutum shida ne suka mutu a farko, amma rahotanni daga asibitin sojoji sun tabbatar da cewar adadin mamatan ya ƙaru zuwa mutum 12.

Wasu mutum 22 sun jikkata, ciki har da biyar da ke cikin mawuyacin hali, kamar yadda jami’ar asibitin sojojin ƙasar ta tabbatar.

Ministan Tsaro, Dokta Cassiel Ato Forson, ya ce an dakatar da ɗaukar na wani ɗan lokaci tare da kafa kwamiti domin binciken musabbabin lamarin, wanda ta bayyana a matsayin abin takaici.

Shugaban ƙasar, John Mahama, ya kai ziyarar jaje ga iyalan waɗanda suka mutu da kuma marasa lafiya, inda ya bayyana cewa gwamnati za ta ɗauki matakan tabbatar da cewa irin wannan lamari ba zai sake faruwa ba.

Rundunar Tsaron Ghana ta miƙa sakon ta’aziyya ga iyalan da abin ya shafa tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kula da waɗanda suka jikkata a asibitin sojoji.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
  • Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau
  • ‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • Super Falconets ta lashe gasar WAFU ta ’yan ƙasa da shekaru 20
  • Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo
  • Troost-Ekong ya gargaɗi Super Eagles kan wasan da za ta fafata da Gabon
  • Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo