Aminiya:
2025-11-14@20:36:22 GMT

Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara

Published: 14th, November 2025 GMT

An kashe wani da ake zargin ɗan bindiga ne, yayin wani artabu da ’yan sanda da ’yan sa-kai suka yi da wasu mahara a Jihar Kwara.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Adekanbi, kusa da garin Bode Saadu.

Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa Mutfwang ya musanta raɗe-raɗin sauya sheƙa zuwa YPP

Rahotanni sun nuna cewa ’yan bindigar sun yada zango a saman wani dutse da ke kallon ƙauyen.

Suna hangar jami’an tsaro sai suka fara harbi ba ƙaƙƙautawa.

’Yan sanda da jami’an sa-kai sun yi artabu tare da tarwatsa maharan, inda wasu daga cikinsu suka tsere da raunin harbin bindiga.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a.

Bayan an artabun, jami’an tsaro sun duba yankin, inda suka samu gawar mutum ɗaya da ake zargin ɗan bindiga ne.

Haka kuma an gano bindiga ƙirar AK-49 da harsasai 32 a wajen.

SP Adetoun, ta ce wannan aikin wani muhimmin ci gaba ne a ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen kawar da masu aikata laifi a jihar.

Ta kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Artabu Kwara mahara

এছাড়াও পড়ুন:

An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe

Gwamnatin Jihar Gombe ta dakatar da wani Hakimi da Dagaci a ƙaramar hukumar Funakaye bayan barkewar rikici tsakanin manoma da makiyaya a yankin.

Rahotanni sun ce rikicin dai ya yi sanadin mutuwar ɗan sanda ɗaya tare da jikkatar wasu jami’an tsaro da dama.

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin kashi 15 na shigo da fetur da dizal Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano

Kwamishinan Shari’a na jihar, Barista Zubairu Muhammad, ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai bayan zaman kwamitin tsaro da aka gudanar ranar Laraba.

Ya ce an dauki matakin dakatarwar ne domin tabbatar da doka da oda, tare da aika sakon gargaɗi ga sauran masu rike da sarautun gargajiya cewa ba za a lamunci sakaci wajen dakile rikice-rikice ba.

“Majalisar ta yi nazari mai zurfi kan lamarin kuma ta nuna damuwa. Gwamnati ba za ta lamunci kai hari ga jami’an tsaro ko hana su gudanar da ayyukansu bisa doka ba. Duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji shi.

Barista Muhammad ya tabbatar da cewa an kama wasu da ake zargi da hannu a harin da aka kai wa jami’an tsaron, kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.

Kwamishinan ya ce kodayake ɗaya daga cikin shugabannin da aka dakatar ya rasa ɗansa a cikin lamarin, hakan bai hana gwamnati ɗaukar mataki ba saboda gazawarsa wajen hana rikicin ya ƙara kamari.

“Rahotanni game da halayen mamacin sun tayar da hankali. Da mahaifinsa, wanda shi ne shugaba a yankin, da ya ɗauki mataki tun da wuri, da ba a kai ga tashin hankali ba. Jagoranci na nufin jarumta da adalci,” in ji shi.

Kwamishinan ya sake jaddada goyon bayan gwamnati ga jami’an tsaro, inda ya yaba da jajircewarsu wajen tabbatar da zaman lafiya wanda ya sa jihar ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da suka fi kwanciyar hankali a ƙasar.

“Gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro don su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa. Duk wani yunƙurin tsoratar da su ko hana su aiki ba za a lamunce shi ba,” in ji shi.

Barista Muhammad ya kuma ambaci rahoton kwamiti ƙarƙashin tsohon Mataimakin Sufeton ’yan sanda na kasa, AIG Zubairu Muazu (mai ritaya), wanda ya binciki tushen rikicin na manoma da makiyaya a jihar.

Kwamishinan ya ce kwamitin ya gano toshe burtalolin kiwo na asali ta hanyar gonaki da gine-gine a matsayin babban abin da ke haddasa rikice-rikicen da ake ta fama da su.

Gwamnatin jihar ta kuma jaddada aniyarta ta kare zaman lafiya tare da yin gargaɗin cewa babu wanda za a rufa wa asiri idan aka same shi da laifin kawo barazana ga tsaro ko hana shari’a gudanar da aikinta yadda ya kamata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma